Babban Labari

Tsohon Kakakin Majalisar Wakilai, Ghali Na’Abba ya kwanta dama

Tsohon Kakakin Majalisar Wakilai, Ghali Na’Abba ya kwanta dama

Daga BASHIR ISAH Allah Ya yi wa tsohon Shugaban Majalisar Wakilai ta Kasa, Alhaji Ghalli Na’abba rasuwa. Duk da dai babu cikakken bayani game da rasuwar tasa, amma majiya mai tushe ta ce marigayin ya rasu ne da misalin karfe 3:00 na daren da ya gabata. A shekarar 1999 ya zama dan majalisa mai wakiltar Kano Municipal a Majalisar Wakilai, inda daga bisani ya samu nasarar zama Kakakin Majalisar. An haifi marigayin ne a 1958 a zuri'ar Alhaji Umar Na’Abba, a yankin Tudun Wada, Kano.
Read More
Kisan bom: Al’ummar Tudun Biri sun yi tutsun zuwa kotu

Kisan bom: Al’ummar Tudun Biri sun yi tutsun zuwa kotu

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Al’ummar ƙauyen Tudun Biri da ke Jihar Kaduna sun yi tutsu bisa ƙarar da aka shigar da sunansu a Babbar Kotun Tarayya Kaduna ta neman Gwamnatin Tarayya ta biya su diyyar Naira biliyan 33 kan kuskuren harin boma-bomai da aka kai, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane sama da 100 tare da jikkata wasu da dama. Dagacin ƙauyen Tudun Biri, Malam Balarabe Garba, ne ya bayyana haka a lokacin da ya kai ziyarar godiya ga Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, inda ya ce, sun samu labarin cewa, wasu sun garzaya kotu a madadinsu.…
Read More
Da Ɗumi-ɗumi: Gwamnati ta amince da cire jami’o’i da takwarorinsu daga tsarin biyan albashi na IPPIS

Da Ɗumi-ɗumi: Gwamnati ta amince da cire jami’o’i da takwarorinsu daga tsarin biyan albashi na IPPIS

Daga BASHIR ISAH Majalisar Zartarwa ta Tarayya (FEC), ta amince da cire jami'o'i da sauran manyan makarantun ƙasar nan daga tsarin biyan albashi na bai-ɗaya, IPPIS. Da wannan, yanzu makarantun da lamarin ya shafa su da kansu za su riƙa kula da biyan albashin ma'aikatansu. Ministan Ilimi, Farfesa Mamman Tahir, shi ne ya bayyana haka ga manema labarai jim kaɗan bayan kammala zaman majalisar a ranar Laraba a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja. Ya ce gwamnati ta yanke shawarar cire manyan makarantu daga tsarin biyan albashi ns IPPIS ɗin ne saboda damuwa da son ganin harkokin makarantun suna gudana…
Read More
Tudun Biri: Sanatoci sun sadaukar da albashinsu na wata guda ga waɗanda harin bom ya shafa

Tudun Biri: Sanatoci sun sadaukar da albashinsu na wata guda ga waɗanda harin bom ya shafa

Daga BASHIR ISAH Baki ɗayan sanatocin Tarayyar Nijeriya su 109 sun yanke shawarar sadaukar da albashinsu na wata guda da ya kai Naira miliyan 109 ga waɗanda iftila'in harin bom ya shafa a Tudun Biri, cikin Ƙaramar Hukumar Igabi, Jihar Kaduna. Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau Jibrin ne ya bayyana haka ranar Lahadi a Fadar Gwamnatin Jihar Kaduna yayin da ya jagoranci tawagar Majalisar Dattawa zuwa jihar don miƙa ta'aziyya da kuma jajantawa. Gwamnan Jihar, Sanata Uba Sani, shi ne ya tarbi tawagar yayin ziyarar. Cikin sanarwar da ya fitar ta hannun hadiminsa Ismail Mudashir, Sanata Barau ya ce…
Read More
Kisan masu mauludi: Za a hukunta masu hannu ciki – Tinubu

Kisan masu mauludi: Za a hukunta masu hannu ciki – Tinubu

*A na cigaba da tir da kisan ’yan mauludi a Kaduna*Za mu biya diyya, inji Gwamnatin Tarayya *Fasahar zamani za ta rage tashin boma-bomai – Amurka ga sojojin Nijeriya Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya tabbatar wa al’ummar ƙasar cewa duk wanda aka samu da hannu a harin bom da aka kai ƙauyen Tudun Biri wanda ya yi sanadiyar mutuwar mutane sama da 90 za a hukunta shi. Shugaban Ƙasar ya kuma bayar da tabbacin cewa, za a kula da duk waɗanda abin ya shafa a ƙarƙashin shirin tallafi na Folako Initiative da za a…
Read More
PDP ga majalisa: Ku yi watsi da ƙudirin kasafin 2024

PDP ga majalisa: Ku yi watsi da ƙudirin kasafin 2024

*”Akwai shifcin gizo da aringizo cikinsa” Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Babbar Jam’iyyar adawa a Nijeriya, PDP, ta roqi Majalisar Dokoki ta Ƙasar, wato Majalisar Dattawa da Majalisar Wakilai da cewa, kada su amince da kasafin kuɗi na 2024, domin cike ya ke maƙil da aringizo, almara da rainin hankali ga talakawa. Sakataren PDP na Ƙasa, Debo Ologunagba, ne ya fitar da wannan sanarwa a ranar Alhamis, kwan ɗaya bayan Shugaba Bola Tinubu ya kammala gabatar da kasafin a gaban gamayyar zauren Majalisar Dattawa da Majalisar Tarayya a Abuja a ranar Laraba. Kasafin na Naira Tiriliyan 27.5 dai PDP…
Read More
Tafiye-tafiye: Ban kashe miliyan N400 ba – Gwamna Dauda

Tafiye-tafiye: Ban kashe miliyan N400 ba – Gwamna Dauda

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya ƙaryata labarin ƙarya da ake yaɗawa na cewa, ya kashe sama da Naira miliyan 400 a balaguro zuwa ƙasashen waje. Rahotanni sun nuna cewa, wata jarida ta yanar gizo ta yi kuskuren ruwaito Gwamna Dauda ya kashe Naira 170,276,294.31 wajen tafiye-tafiye na ƙasa da ƙasa, N221,567,094 kan tafiye-tafiyen cikin gida, N6,929,500.00 kan harkokin tsaro na sirri cikin watanni uku. Sai dai wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar a ranar Alhamis, ta ce wasu vata gari ne suka ƙirƙiri labarin da gangan…
Read More
Da Ɗumi-ɗumi: Kotun Ɗaukaka Ƙara ta sauke Gwamnan Filato

Da Ɗumi-ɗumi: Kotun Ɗaukaka Ƙara ta sauke Gwamnan Filato

Daga BASHIR ISAH Kotun Ɗaukaka Ƙara ta soke Caleb Muftwang na PDP a matsayin halastaccen zaɓaɓɓen Gwamnan Jihar Filato sannan ta ayyana Dr Nentawe na Jam'iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaɓe. Kotun ta yanke hukuncin ne a zaman da ta yi a wannan Lahadin. Alƙalan kotun ƙarƙashin jagorancin Mai Shari'a Williams-Dawodu, sun ayyana ɗan takarar Jam'iyyar APC, Dr. Nentawe Yilwatda, a matsayin halastaccen wanɗa ya lashe zaɓen. Kotun ta umarci Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), da ta janye shahadar lashe zaɓen da ta miƙa wa Mutfwang sannan ta miƙa wa Dr. Yilwatda.
Read More
Ya za ta kaya a shari’ar zaɓen gwamnan Kano?

Ya za ta kaya a shari’ar zaɓen gwamnan Kano?

*Yau Kotun Ɗaukaka Ƙara za ta yanke hukunci Daga MAHDI M. MUHAMMAD Kotun Ɗaukaka Ƙara ta saka yau Juma'a, 17 ga Nuwamba, 2023, a matsayin ranar yanke hukunci kan ƙarar da Gwamnan Jihar Kano ya ɗaukaka, inda yake ƙalubalantar soke nasarar zaɓensa da kotun zaɓen jihar ta yi kwanakin baya. Gwamna Abba Kabir Yusuf na Jam’iyyar NNPP ya garzaya gaban Kotun Ɗaukaka Ƙara ne bayan kotun ƙorafin zave ta Jihar Kano a ranar 20 ga watan Satumba ta rushe nasarar da ya samu a babban zaɓen 2023, inda ta ce abokin takararsa na Jam'iyyar APC, Nasir Yusuf Gawuna, ne halastaccen…
Read More
NLC, TUC sun dakatar da yajin aiki

NLC, TUC sun dakatar da yajin aiki

Daga BASHIR ISAH Ƙungiyar Ƙwadago ta Nijeriya (NLC) da Ƙungiyar 'Yan Kasuwa ta Nijeriya (TUC) da sauran takwarorinsu, sun dakatar da yajin aikin da suka fara tun ran 14 gs Nuwamban 2023. Dakatar da yajin aikin ya biyo bayan ganawar da ƙungiyoyin suka yi da Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara Kan Lamarin Tsaro (NSA), Nuhu Ribadu. Taron wanda ya gudana a ofishin NSA ya samu halartar Shugaban TUC, Festus Osifo; Babban Sakataren NLC, Emmanuel Ugboaja; Ministan Ƙwadago, Simon Lalong da sauransu. NLC ta shiga yajin aiki ne don nuna rashin jin daɗinta kan dukan da aka yi ws shugabanta…
Read More