15
Aug
Daga BASHIR ISAH Gwamnatin Tarayya ƙarƙashin jagorancin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, ta sake maka tsohon Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Godwin Emefiele a kotu inda take tuhumarsa da aikata laifuka 20. Wannan na zuwa ne bayan shigar da buƙatar janye ƙarar "mallakar bindiga ta haramtacciyar hanya" da gwamnatin ta shigar da fari kan Emefiele ɗin a Babban Kotun da ke zamanta a Legas. Daraktan sashen shigar da ƙararraki (DPP) a Ma'aikatar Shari'a ta Ƙasa, Mohammed Abubakar, ya sahaida wa alƙalin kotun, Nicholas Oweibo, cewar buƙatar janye ƙarar daga ɓangaren gwamnati ta taso ne domin ba da damar zurfafa bincike.…