Babban Labari

ASUU ta yi barazanar shiga yajin aikin gama-gari

ASUU ta yi barazanar shiga yajin aikin gama-gari

Ƙungiyar Malaman Jami'o'i (ASUU), ta yi barazanar shiga yajin aiki na gama-gari domin nuna rashin jin daɗinta kan tshin samun majalisar gudanarwa a ɗaukacin Jami'o'in Gwamnatin Tarayya da ke faɗin ƙasa da sauran buƙatu. Ƙungiyar ta ce idan za a iya tunawa, a watan Mayun bara ne gwamnatin ta sauke majalisar gudanarwa na Jami'o'in, tare da cewa duk matakin da ta ɗauka dangane da hakan 'yan Nijeriya su kama gwamnati da laifi. Shugaban ASUU na ƙasa, Farfesa Emmanuel Osodeke ya yi wannan bayani yayin taron manema labarai da ya shirya a sakatariyar ASUU da ke Abuja a ranar Talata.
Read More
Adadin yaran da ba sa tafiya makaranta ya kai miliyan 18 a Nijeriya — UNICEF

Adadin yaran da ba sa tafiya makaranta ya kai miliyan 18 a Nijeriya — UNICEF

Daga BASHIR ISAH Asusun Kula da Ƙananan Yara na Majalisar Ɗinkin (UNICEF) ya koka kan yadda ake samun ƙaruwar yaran da ba sa tafiya makaranta a Nijeriya, tare da cewa, yanzu adadin waɗannan yara ya kai miliyan 18.3. Ya ce wannan adadi ya sa Nijeriya ta zama ƙasar da ta fi kowace ƙasa a faɗin duniya yawan yaran da ba sa tafiya makaranta. Babban Jami'in UNICEF a Bauchi, Dokta Tushar Rane, shi ne ya bayyana haka a wajen taron masu ruwa da tsaki na yini biyun da aka shirya a Gombe kan batun ƙananan yaran da ba sa tafiya makaranta…
Read More
Kotu ta ba da belin Sirika da ‘yarsa kan N100m

Kotu ta ba da belin Sirika da ‘yarsa kan N100m

Daga BASHIR ISAH Babbar Kotun Tarayya mai zamanta a Abuja ta ba da belin tsohon Minista a Gwamnatin Buhari, Hadi Sirika 'yarsa tare da wasu mutum biyu kan kuɗi Naira miliyan 100 da shaidu guda biyu. Idan za a iya tunawa hukumar yaƙi da rashawa ta EFCC ta maka waɗanda lamarin ya shafa a kotu ne bisa zargin laifuka shida. EFCC na zargin Sirika da yin amfani da damar ofishins wajen aikata ba daidai ba tsakanin Afrilun 2022 da Maris, 2023 a Abuja. Kazalika, hukumar tana zargin tsohon ministan da yin sama da faɗi da biliyan N1.3 wajen ba da…
Read More
Rashin kyawun jirgi ya hana Shettima tafiya taro a Amurka

Rashin kyawun jirgi ya hana Shettima tafiya taro a Amurka

Daga BASHIR ISAH Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima, ba zai samu halartar babban taron kasuwanci da ke gudana a Amurka ba sakamakon rashin kyawun Jirgin saman Shugaban Ƙasa. Taron wanda haɗin gwiwa ne tsakanin Amurka da Afirka, an shirya Shettima zai halarta ne a madadin Shugaba Bola Tinubu, wanda zai gudana daga ran 6 zuwa 9 ga Mayu, 2024. Sai dai kuma, ala tilas Shettima ya fasa wannan tafiyar saboda rashin kyawun jirgin da zai ɗauke su zuwa Amurka. Mai magana da yawun Mataimakin Shugaban Ƙasar, Stanley Nkwocha, ya faɗa a ranar Litinin cewa, matsalar gyara da jirgin saman da…
Read More
Ƙarancin ruwa na jikkata majinyata a asibitin Dutse

Ƙarancin ruwa na jikkata majinyata a asibitin Dutse

*Gwamnatin Jigawa ta samar da inji – Shugaban asibitin Daga UMAR AKILU MAJERI a Dutse Ƙarancin ruwan sha ya addabi babban asibitin kwanciya na Dutse, Babban Birnin Jihar Jigawa, wato Dutse General Hospital, lamarin da ya sa marasa lafiya da masu zaman jiyya yin gararambar neman ruwan sha a unguwannin Maranjuwa, Fagoji Bakwato da bakin kasuwar ’yan Tifa da ke birnin na Dutse. Kamar yadda binciken Wakilin Blueprint Manhaja ya nuna, ta kai ta kawo marasa lafiya da masu zaman jiyya sun koma yin alwala da ruwan leda da ake kira da ‘pure water’ na Naira 20 ƙwaya ɗaya da…
Read More
Tudun Biri: Sojoji 12 sun gurfana gaban kotunsu bayan kammala bincike

Tudun Biri: Sojoji 12 sun gurfana gaban kotunsu bayan kammala bincike

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Rundunar Sojojin Nijeriya ta bayyana cewa, ta kammala binciken da aka daɗe ana dakon sakamakonsa kan bom ɗin da aka jefa bisa kuskure kan mutanen ƙauyen Tudun Biri a Ƙaramar Hukumar Igabi da ke Jihar Kaduna. Ta kuma ce, sojojin da aka samu da laifi a kai harin, za su gurfana a gaban kotun soji, domin fuskantar hukunci. Daraktan yaɗa labarai na hedikwatar tsaron Nijeriya, Edward Buba, ne ya bayyana haka a taron manema labaran da aka gudanar a Abuja. A Disambar bara ne wani jirgin sojoji ya jefa bom kan mutanen da ke bikin Maulidi,…
Read More
Tinubu ya taya Idris murnar zagayowar ranar haihuwarsa

Tinubu ya taya Idris murnar zagayowar ranar haihuwarsa

Daga BASHIR ISAH Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya taya Ministan Labarai da Wayar da Kan 'Yan Ƙasa, Mohammed Idris, murnar zagayowar ranar haihuwarsa. Hakan na ƙunshe ne cikin sanarwar da mai magana da yawun Shugaban Ƙasa, Ajuri Ngelale, ya fitar a ranar Laraba. Sanarwar ta ce, Ministan hadimin gwamnati ne wanda ya zo a daidai lokacin da ake buƙatarsa. Ta ƙara da cewa, Ministan wanda mawallafi ne kuma ɗan siyasa, yana aiki da ƙwarewa a matsayinsa na Ministan Labarai da Wayar da Kan 'Yan Ƙasa. Haka nan, ta ce Idris na daga cikin 'yan sahun gaba a fagen yaɗa labarai…
Read More
1 ga Mayu sabon albashi mafi ƙaranci zai fara aiki – Gwamnati

1 ga Mayu sabon albashi mafi ƙaranci zai fara aiki – Gwamnati

*Ba mu amince da ƙarin albashin kashi 35 ba — NLC Daga BSHIR ISAH Gwamnatin Tarayya ta ba da tabbacin cewa sabon albashi mafi ƙaranci zai fara aiki daga 1 ga Mayu. Kodayake, Gwamnatin ta ce kwamitin da ke da ruwa da tsaki kan batin ƙarin albashin bai kammala aikinsa ba tukuna. Ƙaramin Ministan Ƙwadago, Nkeiruka Onyejeocha, ita ce ta yi wannan babayin a wajen taron bikin Ranar Ma'aikata da aka shirya ranar Laraba a Abuja. Ta ce abin takaici ne ƙarin albashin bai kammalu ba zuwa wannan lokaci, amma cewa ana ci gaba da tattaunawa domin tabbatar dukkanin bayanai…
Read More
Emefiele ba ya bayar da kwangila sai da cin hanci, in ji shaida

Emefiele ba ya bayar da kwangila sai da cin hanci, in ji shaida

Daga BASHIR ISAH Mutum na biyu da ke ba da shaida a kan shari'ar da tsohon Gwamnan CBN, Godwin Emefiele ke fuskanta, ya bayyana wa Kotu ƙarara cewa lallai Emefiele ba ya ba da kwangila ba tare da ya karɓi cin hanci ba. John Ayo wanda ya kasance tsohon Darakta na Sashen Labarai na CBN, ya bayyana haka ne ga Babban Kotun da ke zamanta a Ikeja, Jihar Legas. Ya bayyana haka ne a lokacin da yake ba da shaida a gaban Alƙali Rahman Oshodi yayin zaman da kotun ta yi a ranar Litinin. Emefiele na fuskantar shari'a ne kan…
Read More