Babban Labari

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu ya dakatar da shugaban EFCC, Bawa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu ya dakatar da shugaban EFCC, Bawa

Shugaban Ƙasa Bola Tinubu, ya dakatar da Shugaban Hukumar EFCC, AbdulRasheed Bawa, har baba-ta-gani. An dakatar da Bawa ne domin samun damar gudanar da bincike kan zarge-zargen da ake yi masa na yin amfani da ofishinsa wajen aikata ba daidai ba. Sanarwar da Daraktan Yaɗa Labarai na Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya, Willie Bassey, ya fitar ta ce, an dakatar da Bawa ne saboda zargin da ake yi masa na keta alfarmar ofishinsa. “An umarci Bawa da ya gaggauta miƙa ragamar ofishinsa ga Daranktan Ayyuka a hukumar, wanda shi zai ci gaba da kula da hukumar zuwa lokacin da za a…
Read More
Akpabio ya zama Shugaban Majalisar Dattawa

Akpabio ya zama Shugaban Majalisar Dattawa

Daga BASHIR ISAH An zaɓi ɗan takarar Shugaban Majalisar Dattawa na Jam'iyyar APC, Godswill Akpabio, a matsayin Shugaban Majalisar Dattawa. Akpabio ya lashe zaɓen da ƙuri'u 63 inda ya doke Sanata Abdulaziz Yari wanda ya tsira da ƙuri'u 46. Akawun Majalisar Tarayya, Sani Tambuwal, shi ne ya sanar da sakamakon zaɓen. Tambuwal ya ce sanatoci 107 ne suka kaɗa ƙuri'a. Sanata Ali Ndume ne ya zaɓi Akpabio don takarar Shugaban Majalisar, yayin da Sanata Adeola Olamilekan, daga Jihar Ogun, ya mara masa baya.
Read More
Gabanin zaɓen shugabannin majalisa… A na zargin ƙulla maƙarƙashiyar kama Yari

Gabanin zaɓen shugabannin majalisa… A na zargin ƙulla maƙarƙashiyar kama Yari

*Ƙungiya ta ja hankalin Tinubu da APC*Kotu ta tsawaita wa’adin hana kama shi*Za a ƙaddamar da Majalisa ta 10 ranar Talata Daga NASIR S. GWANGWAZO da MAHDI M. MUH’D Rahotanni sun nuna cewa, jami’an tsaron Nijeriya suna ƙulle-ƙullen kama tsohon Gwamnan Jihar Zamfara, Abdul’aziz Yari, su tsare shi har sai bayan ƙaddamar da Majalisar Dokokin Nijeriya ta 10 da za a yi ranar Talata mai zuwa, don tabbatar da cewa, bai samu damu tsaya wa takarar shugabancin Majalisar Dattawa ba. Wannan zargin ya fito ne daga bakin Shugaban Ƙungiyar Matasan Yankin Arewa Maso Gabas (North East Youth Organisation Forum), Alhaji…
Read More
Cire tallafin mai: Gwamnoni sun yi wa Tinubu mubaya’a

Cire tallafin mai: Gwamnoni sun yi wa Tinubu mubaya’a

Daga BASHIR ISAH Gwamnoni 36 a faɗin ƙasa, sun bayyana goyon bayansu ga Shugaban Ƙasa Bola Tinubu dangane da batun cire taffin mai. Gwamnonin sun bayyana haka ne yayin ganawar da Shugaban Ƙasar ya yi da Ƙungiyar Gwamnoni (NGF), ranar Laraba a fadarsa da ke a Abuja. Gwamnonin ƙarƙashin jagorancin Gwamna AbdulRahman AbdulRazaq na Jihar Kwara, sun bayyana farin ciki da gamsuwarsu game da matakin cire tallafin mai da Shugaba Bola ya ɗauka. Kazalika, sun bai wa Tinubun tabbaci tare da ɗaukar masa alƙawarin za su yi aiki tare a kan haka. Tun farko da yake jawabi, Shugaba Tinubu ya…
Read More
Batun cire tallafin mai ya rikita ƙasa

Batun cire tallafin mai ya rikita ƙasa

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Tun bayan da zaɓaɓɓen sabon Shugaban Nijeriya, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, ya furta kalaman cewa, an kawo ƙarshen biyan tallafin man fetur da Gwamnatin Tarayya ke yi a ƙasar, al’amura suka soma rikicewa, inda kace-nace ya ɓalle kan batun, sannan kayayyaki suka yi mummunan tashin gwauron zabo, wanda ba a tava ganin irinsa ba a nan kusa, musamman ma farashin litar man fetur ya ninka kusan sau uku. Shugaba Tinubu ya yi wannan furuci ne a lokacin da ya ke gabatar da jawabinsa na farko a matsayin Shugaban Ƙasa ranar Litinin, 29 ga Mayu,…
Read More
Cire Tallafin Mai: Farashin fetur ya cilla zuwa N700 kan lita guda

Cire Tallafin Mai: Farashin fetur ya cilla zuwa N700 kan lita guda

Daga BASHIR ISAH Rahotanni daga sassan Nijeriya sun ce, a halin da ake ciki farashin fetur ya ƙaru zuwa Naira 700 kan kowace lita a wasu sassan ƙasar. Wannan ya biyo bayan sanar da cire tallafin mai baki ɗaya da sabon Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi a jawbinsa ga ‘yan ƙasa jim kaɗan da rantsar da shi a ranar Litinin da ta gabata. Binciken Manhaja ya gano cewar, matakin cire tallafin da Shugaba Tinubu ya ɗauka ya haifar da ƙarin farashin mai da kashi 100 zuwa 250, inda a yanzu ake sayar da lita guda na fetur tsakanin…
Read More
Ƙarancin mai ya kunno kai sa’o’i bayan da Shugaba Tinubu ya sanar da cire tallafin mai

Ƙarancin mai ya kunno kai sa’o’i bayan da Shugaba Tinubu ya sanar da cire tallafin mai

Da alama layukan ababen hawa a gidajen mai ya dawo a Jihar Legas sa'o'i bayan da Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya sanar da cire tallafin mai. Bayanai sun ce an ga cinkoson ababen hawa a gidajen mai ɗin NNPC a yankunan Ikeja da Alausa waɗanda ke jiran su sha mai. Ya zuwa haɗa wannan labari, an ga da daman gidan mai masu zaman kansu a yankunan ba su sayar da mai. A jawabinsa, Shugaba Tinubu ya ce masu ƙumbar susa kaɗai ke amfna da tallafin mai amma ban da talakawa. Ya ce, “Mun yaba da ƙoƙarin gwamnati mai barin gado…
Read More
Buhari da Tinubu: Ta faru ta ƙare!

Buhari da Tinubu: Ta faru ta ƙare!

*Yayin da Tinubu ya kammala shirin amsar mulki…*Buhari ya yi sabbin naɗe-naɗe 33 kwanaki shida kafin miƙa mulki*Dalilin da ya sa Buhari ke ta ɗaukar matakai – Fadar Shugaban Ƙasa *Ana shirin kawo cikas ga bukukuwan miƙa mulki a jihohi da ƙasa, inji DSS*Sa'o'i kafin miqa mulki Buhari ya umarci ministocinsa su cigaba da aikinsu*Ƙananan ministoci ba su da amfani a gwamnatin Buhari – Keyamo Daga MAHDI M. MUHAMMAD A ranar Litinin, 29 ga Mayu, 2023, gwamnatin sabon Shugaban Nijeriya mai jiran gado, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, za ta fara aiki a matsayin halastacciyar zaɓaɓɓiyar gwamnatin farar hula, yayin da…
Read More
Za a jinginar da filayen jirgin saman Kano da Abuja

Za a jinginar da filayen jirgin saman Kano da Abuja

*Za a ƙara ciwo bashin Dala miliyan 800*Za a nutsar da kuɗin a shirin rage raɗaɗin cire tallafin fetur Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnatin Nijeriya ta amince a jinginar da filin jirgin saman Nnamdi Azikiwe da ke Abuja da kuma Malam Aminu Kano da ke Kano. Gwamnati ta amince da wannan mataki ne a taron majalisar koli da aka gudanar ranar Laraba a Abuja. Ministan Sufirin Jiragen Sama a Nijeriya, Hadi Sirika, ya shaida wa BBC cewa za a jinginar da filin jirgin Abuja na shekara 20, sannan na Kano na tsawon shekara 30. Sirika ya ce taron…
Read More