Babban Labari

Don kare Nijeriya daga faɗawa fatara ya sa na cire tallafin fetur — Tinubu

Don kare Nijeriya daga faɗawa fatara ya sa na cire tallafin fetur — Tinubu

Daga BASHIR ISAH Shugaban Ƙasa, Bola Tinubu, ya jaddada cewa matakin cire tallafin fetur da gwamnatinsa ta ɗauka abu ne da ya zama wajibi don hana ƙasar faɗawa cikin fatara. Tinubu ya bayyana haka a ne sa'ilin da yake jawabi a wajen taron tattalin arzikin duniya da ke gudana a birnin Riyadh na ƙasar Saudiyya a ranar Lahadi. Ya ce akwai buƙatar cire tallafin na fetur domin sake farfaɗo da tattalin arzikin ƙasar. Ta bakinsa, “Ga Nijeriya, mun yi amannar haɗin gwiwar tattalin arziki da haɗa kai ya zama dole don samar da kwanciyar hankali a sauran ƙasashen duniya. "Game…
Read More
Ruwan sama da ’yan bindiga sun ruɗa Neja

Ruwan sama da ’yan bindiga sun ruɗa Neja

*Jama’a na tserewa saboda janye sojoji*Fursunoni 118 sun tsere daga kurkukun Suleja Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Jama’a sun yi hijira bayan an rufe sansanin soji da kuma janye sojoji da ke aikin samar da tsaro a ƙauyen Allawa da ke Ƙaramar Hukumar Shiroro ta Jihar Neja. Wannan ya zo ne a daidai lokacin da fursunoni guda 118 suka arce daga gidan yarin Suleja sakamakon mamakon ruwan saman da ya rikita gidan kurkukun. A ranar Alhamis ne sojojin Nijeriya suka rufe sansaninsu bayan bayar sa rahoton yi mu su kisan kiyashi, wanda ya janyo firgici a tsakanin al’ummar yankin…
Read More
Ministan Yaɗa Labarai ya kafa Kwamitin Kare Haƙƙoƙin Nakasassu

Ministan Yaɗa Labarai ya kafa Kwamitin Kare Haƙƙoƙin Nakasassu

Daga WAKILINMU Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kan Jama’a, Mohammed Idris, ya ba da umarnin kafa wani kwamiti mai mambobi biyar domin tsara aiki da hukumar nakasassu ta ƙasa domin wayar da kan jama’a game da ‘yancin nakasassu da kuma damar da suke da a rayuwa. Mataimaki na musamman ga ministan,Rabiu Ibrahim ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya raba wa manema labarai. Ministan ya bayar da wannan umarnin ne a ranar Laraba, a babban birnin tarayya Abuja, lokacin da ya karbi baƙuncin babban sakataren hukumar nakasassu na ƙasa, Dr. James Lalu, a wata ziyarar ban girma…
Read More
Zan yi murabus muddin ba a hukunta Yahaya Bello ba — Shugaban EFCC

Zan yi murabus muddin ba a hukunta Yahaya Bello ba — Shugaban EFCC

Daga BASHIR ISAH Shugaban Hukumar Yaƙi da Rashawa ta EFCC, Ola Olukoyede, ya lashi takobin bin diddigin zargin almundahanar Naira biliyan 80.2 da ake yi wa tsohon Gwamnan Jihar Kogi, State Yahaya Bello har zuwa ƙarshe. Olukoyede ya furta haka ne a hirar da ya yi da manema labarai a Babban Ofishin hukumar da ke Abuja, inda ya ce babu makwa zai yi murabus muddin ba a hukunta Bello ba. "Idan ni da kaina ban ga ƙarshen wannan binciken game da Yahaya Bello ba, zan a jiyen' muƙamina a matsayin Shugaban EFCC Chairman,” in ji Olukoyede. Ya ce Bello ya…
Read More
EFCC na son tsoma sojoji a dambarwa EFCC da Yahaya Bello

EFCC na son tsoma sojoji a dambarwa EFCC da Yahaya Bello

Daga MAHDI M. MUHAMMAD A ranar Larabar da ta gabata ne dai tsohon Gwamnan Jihar Kogi, Alhaji Yahaya Bello, ya yi kira ga Shugaban Qasa Bola Tinubu da ya ja wa Hukumar Yaƙi da Masu yi wa Tattalin Arzikin Ƙasa Zagon Ƙasa ta EFCC kunne bisa zargin ƙin bin umarnin kotu, wacce ta hana a kama shi. To, sai dai kuma a ranar Alhamis Hukumar ta EFCC ta bayyana cewa, ta na duba yiwuwar tsoma rundunar sojojin Nijeriya a cikin dambarwar, don kamo shi ɗin. Tsohon gwamnan, a wata sanarwa da jami’in yaɗa labaransa, Mista Onogwu Muhammed, ya fitar a…
Read More
Da Ɗumi-ɗumi: EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo kan almundahanar N80.2bn

Da Ɗumi-ɗumi: EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo kan almundahanar N80.2bn

Daga BASHIR ISAH Hukumar Yaƙi da Rashawa (EFCC) ta ce tana neman tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello, kan zargin tafka almundahanar Naira biliyan N80.2. Hukumar ta bayyana hakan ne a wani saƙo da ta wallafa a shafinta na soshiyal midiya da yammacin ranar Alhamis. Sanarwar ta ce, “EFCC na neman tsohon Gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Bello, ruwa a jallo bisa laifuka masu alaƙa da almundahar kuɗi da ya biliyan N80.2. "Duk wanda ke da masaniyar inda yake ya hanzarta sanar da hukumar ko kuma ofishin 'yan sanda mafi kusa." Wannan na zuwa ne sa'o'i bayan da Babban Lauyan Ƙasa…
Read More
Tinubu ya ba da umarnin saka ɗaliban NOUN a tsarin NYSC

Tinubu ya ba da umarnin saka ɗaliban NOUN a tsarin NYSC

Daga BASHIR ISAH Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya umarci Ma'aikatar Ilimi ta Ƙasa da ta saka ɗaliban da suka kammala karatu a Jami'ar National Open University (NOUN) a tsarin yi wa ƙasa hidima da aka fi sani da NYSC a taƙaice. Haka nan, Shugaban ya amince a lamunce wa ɗaliban da suka kammala NOUN halartar Makarantar Lauyoyi, wato Law School domin. Tinubu ya ɗauki wannan mataki ne domin samun daidaito wajen baiwa 'yan ƙasa damar cin gajiyar damammakin da ake da su a ƙasa. Shugaba Tinubu ya bayyana haka yayin da yake jawabi a wajen taron bikin yaye ɗalibai karo…
Read More
An buƙaci Tinubu ya ja kunnen EFCC kan yi wa doka karan-tsaye

An buƙaci Tinubu ya ja kunnen EFCC kan yi wa doka karan-tsaye

Daga BASHIR ISAH An yi kira ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu kan ya ja kunnen Hukumar Yaƙi da Rashawa ta Ƙasa (EFCC) bisa karan-tsayen da take yi wa doka wajen gudanar da harkokinta. An buƙaci Tinubu ya taka wa EFCCn burki ne bayan da ta yi yunƙuri cafke tsohon Gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Bello, duk da cewa a baya umarnin kotu ta haramta mata hakan. Idan za a iya tunawa, a ranar 9 ga Fabrairu, 2024, Babbar Kotun da ke zamanta a Lokoja, ta yanke hukunci kan ƙara mai lamba HCL/68M/2024 tsakanin Alhaji Yahaya Bello da EFCC, inda ta…
Read More
Da Ɗumi-ɗuminsa: Kotu ta tabbatar da dakatarwar da aka yi wa Ganduje daga APC

Da Ɗumi-ɗuminsa: Kotu ta tabbatar da dakatarwar da aka yi wa Ganduje daga APC

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Babbar Kotun Jihar Kano mai Lamba 4 dake zaman ta a kan titin Mila, ta tabbatar da dakatarwar da wasu shugabannin Jam'iyyar APC a Mazaɓar Ganduje suka yi wa Shugaban Jam'iyyar na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje daga jam'iyyar. Alƙalin Kotun, Justice Usman Malam Na'abba ne ya tabbatar da hakan ta cikin wata takardar da masu ƙara suka nema, ba tare da sanar wa ɓangaren waɗanda suke ƙara ba wato (Motion Ex parte). Haladu Gwanjo da Laminu Sani ne suka shigar da ƙarar, inda suka yi ƙarar ɓangarori huɗu waɗanda suka haɗar da Jam'iyyar APC, Kwamitin…
Read More
Bayan shekara 10 da sace ‘yan matan Chibok: Wani abu da ya kamata a sani

Bayan shekara 10 da sace ‘yan matan Chibok: Wani abu da ya kamata a sani

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Jaridar News Point Nigeria ta samu damar haɗuwa da Lisu a sirrance, yayin da ta ce wasu na ƙoƙarin hana ta magana da ‘yan jarida. Lisu na ɗaya daga cikin 'yan mata 276 da aka sace daga makarantar sakandare ta 'yan mata a garin Chibok shekaru goma da suka wuce - satar da ta girgiza duniya kuma ta haifar da zangar-zangar neman a dawo da 'yan matan mai taken: #BringBackOurGirls, wanda har ya haɗa da uwargidan tsohon Shugaban Ƙasar Amurka, Michelle Obama. Sama da 180 ne dai suka kuɓuto ko kuma aka sake su,…
Read More