Babban Labari

’Yan bindiga sun bi Sarkin Musulmi ranar sallah

’Yan bindiga sun bi Sarkin Musulmi ranar sallah

*Sun miƙe ƙafa a bainar jama’a Daga NASIR S. GWANGWAZO a Abuja Wasu dandazon ’yan ta'addar daji sun miƙe ƙafa a lokacin Ƙaramar Sallah da a ka gudanar ranar Larabar da ta gabata, inda suka fito suka gudanar da sallar idi tare da sauran bukukuwa a bainar jama'a a Jihar Zamfara da ke yankin Arewa Maso Yammacin Najeriya. Bikin sallar ’yan bindigar daji ya zo ne a daidai lokacin da wasu malamai su ka bijire wa umarnin Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar III, na sauke azumin watan Ramadan a ranar Laraba. Sarkin Musulmi ya sanar da cewa, ba…
Read More
Tinubu ya nuna alhini kan rasuwar Saratu Giɗaɗo

Tinubu ya nuna alhini kan rasuwar Saratu Giɗaɗo

Daga BASHIR ISAH Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya nuna alhininsa dangane da rasuwar jaruma a masana'antar shirya finafinai ta Kannywood, Saratu Giɗaɗo wadda aka fi dani da Daso. Hakan na ƙunshe ne cikin sanarwar da Fadar Shugaban Ƙasa ta fitar mai ɗauke da kwanan wata 10 ga Afrilu da kuma sa hannun mai magana da yawun Shugaban Ƙasa, Ajuri Ngelale. Tinubu ya yi amfani da wannan dama wajen miƙa ta'aziyya ga 'yan uwan da abobakan aiki da masoyan marigayiyar da ke sassa daban-daban. Tinubu ya bayyana rasuwar jarumar mai shekara 56 a matsayin babban rashi ga ƙasa baki ɗaya. Ya…
Read More
’Yan Nijeriya sun kaɗu da ƙarin kuɗin lantarki

’Yan Nijeriya sun kaɗu da ƙarin kuɗin lantarki

•NLC da CHRIceD sun ce akwai rashin tausayi a ƙarin kuɗin*Ba kowa ƙarin zai shafa ba, cewar gwamnati*Ƙarin zai haifar da satar wuta, inji tsohon jami'in NERC Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja A daidai lokacin da al'ummar Nijeriya ke fama da raɗaɗin tashin farashin kayayyakin masarufi da tsadar rayuwar da, sai ga shi Hukumar Kula da Wutar Lantarki ta Nijeriya (NERC) ta fitar da sanarwar amincewa da ƙarin kuɗin wutar lantarki ga kwastomomin da ke ƙarƙashin rukunin samun wuta na Band A, wato waɗanda suka fi samun wutar lantarki. A wani taron manema labarai a wannan Larabar a Abuja,…
Read More
‘A Legas Tinubu zai yi Ƙaramar Sallah’ – Fadar Shugaban Ƙasa

‘A Legas Tinubu zai yi Ƙaramar Sallah’ – Fadar Shugaban Ƙasa

Daga BASHIR ISAH A wannan Lahadin ake sa ran Shuganq Ƙasa Bola Tinubu zai bar birnin tarayya Abuja zuwa Legas gabanin bikin Ƙaramar Sallah na bana. Kakakin Shugaban Ƙasa, Ajuri Ngelale, shi ne ya bayyana haka a wata sanarwa mai taken 'Shugaba Tinubu zai Idil Fiɗr a Legas' wadda ya fitar a ranar Asabar. A cewar Ngelale, “Yayin bikin wanda ke nuni da ƙarewar watan Ramadan, Shugaban zai yi wa Nijeriya addu'o'i tare da ahalinsa." Sai dai sanarwar ba ta fayyace ranar Tinubun zai koma Abuja ba, amma cewa Shugaban zai ci gaba da gudanar harkokinsa lokacin hutun bikin sallar…
Read More
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu ya rattaɓa hannu kan Dokar Bai wa Ɗalibai Rancen Karatu

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu ya rattaɓa hannu kan Dokar Bai wa Ɗalibai Rancen Karatu

Daga BASHIR ISAH A ranar Laraba Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya rataɓɓa hannu kan Dokar Bai wa Ɗalibai Rancen Karatu ta 2024. Da wannan, sabuwar dokar za ta fara aiki ke nan, inda za ta bai wa ɗalibai a manyan makarantu zarafin samun rance daga gwamnati domin gudanar da harkokin karatunsu. Tinubu ya sanya wa dokar hannu ne bayan da Majalisar Tarayya ta nazarci rahoton Kwamitin Kula da Manyan Makarantu da kuma asusun TETFund.
Read More
Kisan Okuama: Mun ci alwashin adalci ga sojojin da aka kashe – DHQ

Kisan Okuama: Mun ci alwashin adalci ga sojojin da aka kashe – DHQ

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Hedikwatar Tsaron Nijeriya ta ci alwashin cewa, ba za ta gajiya ba har sai an kama waxanda suka kashe sojoji 17 a Okuama da ke jihar Delta tare da gurfanar da su a gaban shari’a bisa ga dokar Nijeriya. Daraktan yaɗa labarai na tsaro, Manjo Janar Edward Buba ne ya bayyana haka a lokacin da yake yi wa manema labarai qarin haske kan ayyukan soji da ke gudana a sassan ƙasar nan a Abuja, babban birnin Nijeriya. Janar Buba ya ce "an saki sunayen mutane takwas da ake nema ruwa a jallo ciki har…
Read More
Yadda sabbin gwamnoni 13 suka kinkimi bashin N226.8bn a cikin wata shida – DMO

Yadda sabbin gwamnoni 13 suka kinkimi bashin N226.8bn a cikin wata shida – DMO

Daga BASHIR ISAH Bayabnan da Manhaja ta tattaron sun ce, a jimilIance wasu sabbin gwamnoni su 13 sun ci bashi da ya kai Naira Biliyan 226.8 a cikin watanni shida da suka yi a ofis. Wannan bashin kuwa ya shafi wanda gwamnonin suka ci a gida da kuma ƙetare. Binciken News Point Nigeria ya gano cewa, wasu gwamnonin jihohi 16 kuma, basussukan da suka ciyo ya ƙaruwa da Naira Biliyan 509.3. An yi lissafin basussukan ƙetaren ne kan lissafin N889 kan $1 kamar yadda Ofishin Kula da Basussuka (DMO) ya nuna. Rahoton DMO ya ce an tattaro bayanan basussukan ne…
Read More
Da Ɗumi-ɗumi: Gwamnatin Tinubu ta ware N90bn don cikata wa maniyyata kuɗin Hajji

Da Ɗumi-ɗumi: Gwamnatin Tinubu ta ware N90bn don cikata wa maniyyata kuɗin Hajji

Daga BASHIR ISAH Gwamnatin Tarayya ƙarƙashin jagorancin Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ta ware Naira biliyan 90 domin cikata wa maniyyata kuɗin Hajjin Bana. Tallafin na zuwa ne biyo bayan ƙarin kuɗin Hajji da aka yi bayan sama da Naira miliyan huɗu da maniyyatan suka yi da farko. A farkon wannan makon ne Hukumar Hajji ta Ƙasa (NAHCON) ta ba da sanarwar cewa, an yi ƙarin kuɗin Hajjin bana da Naira Miliyan 1.9 wanda kuma ake buƙatar kowane maniyyaci ya biya a cikin ƙankanin lokaci ko kuma ya haƙura da tafiya Hajji bana. Tun bayan sanarwar ƙarin da NAHCON ta yi,…
Read More
Sojoji sun ga bayan Dogo Gide

Sojoji sun ga bayan Dogo Gide

Daga BASHIR ISAH Rahotanni sun ce dakarun ƙasar Nijar sun ga bayan gawurtaccen ɗan bindigar nan, Dogo Gide, na mayaƙan ANSARU da sauran ƙungiyoyin 'yan ta'adda. MANHAJA ta kalato cewar, Dogo Gide ya mutu ne sakamakon raunin da ya ji biyo bayan musayar wutar da aka yi tsakanin rundunar haɗin gwiwa ta Operation Hadarin Daji (OPHD) a dajin Madada da yankin Ƙaramar Hukumar Maru a ranar 12 ga Maris, 2024. An ce duk da raunin da aka yi injuries, Dogo Gide, sai da aka san yadda aka yi aka saci jiki aka shigar da shi asibiti a yankin Mabera a…
Read More
Yanzu-Yanzu: Kotu ta yanke wa ɗan China hukuncin kisa kan kisan Ummita a Kano

Yanzu-Yanzu: Kotu ta yanke wa ɗan China hukuncin kisa kan kisan Ummita a Kano

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Babbar Kotun Jihar Kano, ta yanke wa ɗan Chinan nan, Frank Geng Quarong hukuncin kisa ta hanyar rataya. Mai Shari’a Sunusi Ado Ma’aji ne ya yanke masa hukuncin, bayan tabbatar da hujjojin da masu gabatar da ƙara suka yi a gaban kotun. Idan za a iya tunawa Manhaja ta rawaito tun a ranar 16 ga watan Satumba 2022, Frank Geng, ya hallaka Ummita a unguwar Janbulo da ke jihar Kano.
Read More