09
Jun
*Ƙungiya ta ja hankalin Tinubu da APC*Kotu ta tsawaita wa’adin hana kama shi*Za a ƙaddamar da Majalisa ta 10 ranar Talata Daga NASIR S. GWANGWAZO da MAHDI M. MUH’D Rahotanni sun nuna cewa, jami’an tsaron Nijeriya suna ƙulle-ƙullen kama tsohon Gwamnan Jihar Zamfara, Abdul’aziz Yari, su tsare shi har sai bayan ƙaddamar da Majalisar Dokokin Nijeriya ta 10 da za a yi ranar Talata mai zuwa, don tabbatar da cewa, bai samu damu tsaya wa takarar shugabancin Majalisar Dattawa ba. Wannan zargin ya fito ne daga bakin Shugaban Ƙungiyar Matasan Yankin Arewa Maso Gabas (North East Youth Organisation Forum), Alhaji…