18
Feb
Daga MUHAMMAD AL-AMEEN, Maiduguri Ɗan takarar Shugaban Ƙasa a Jam'iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu tare da mataimakinsa, Sanata Kashim Shettima da wasu gwamnoni biyar sun yi wa Maiduguri, babban birnin Jihar Borno tsinke domin gudanar da yaƙin neman zaɓe. Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, da takwarorinsa na jihohin Yobe da Gombe, haɗi da jiga-jigan gwamnatin Jihar Borno, su ne tarbi tawagar ɗan takarar da ƙusoshin Jam'iyyar APC yayin gangin da ya gudana ran Asabar. Jim kaɗan da saukarsa a Maiduguri, Tinubu da jiga-jigan jam'iyyar APC suka shiga tattaunawa ta musamman da masu ruwa da tsaki a babban ɗakin taro…