Siyasa

Jirgin yaƙin neman zaɓen Tinubu/Shettima ya sauka Borno

Jirgin yaƙin neman zaɓen Tinubu/Shettima ya sauka Borno

Daga MUHAMMAD AL-AMEEN, Maiduguri Ɗan takarar Shugaban Ƙasa a Jam'iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu tare da mataimakinsa, Sanata Kashim Shettima da wasu gwamnoni biyar sun yi wa Maiduguri, babban birnin Jihar Borno tsinke domin gudanar da yaƙin neman zaɓe. Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, da takwarorinsa na jihohin Yobe da Gombe, haɗi da jiga-jigan gwamnatin Jihar Borno, su ne tarbi tawagar ɗan takarar da ƙusoshin Jam'iyyar APC yayin gangin da ya gudana ran Asabar. Jim kaɗan da saukarsa a Maiduguri, Tinubu da jiga-jigan jam'iyyar APC suka shiga tattaunawa ta musamman da masu ruwa da tsaki a babban ɗakin taro…
Read More
Ƙarancin Naira da man fetur barazana ce ga takarar Tinubu – Gbajabiamila

Ƙarancin Naira da man fetur barazana ce ga takarar Tinubu – Gbajabiamila

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Kakakin Majalisar Wakilai, Femi Gbajabiamila ya danganta matsalar da ake fuskanta a halin yanzu na ƙarancin man fetur da ƙarancin Naira ka iya daƙile nasarar ɗan takarar Shugaban Ƙasa na Jam’iyyar APC, Bola Tinubu na cin zaɓen ranar 25 ga watan Fabrairu. Gbajabiamila ya bayyana haka ne a Legas ranar Talata a lokacin ƙaddamar da shirin raba motocin sufuri mai taken: ‘Gbaja Ride’ ga mazaɓarsa ta Surulere. Motocin bas guda 35 masu saukin farashi za su riƙa bin hanyoyi daban-daban a Surulere da kewaye. “A matsayina na wakilinku kuma mai magana da yawunku, Ina…
Read More
APC ta dakatar da ‘yar takarar gwamnanta a Adamawa

APC ta dakatar da ‘yar takarar gwamnanta a Adamawa

Daga BASHIR ISAH Shugabancin Jam'iyyar APC na Ƙaramar Hukumar Yola ta Kudu a Jihar Adamawa ta dakatar da mai yi wa jam'iyyar takarar gwamna a jihar, Sanata Aishatu Ahmed Dahiru Modibbo (Binani), daga jam'iyyar. Wasiƙar dakatarwar wadda ta samu sa hannun jami'an jam'iyyar 21, ta nuna an ɗauki matakin dakatar da Binani na tsawon wata shida daga jam'iyyar ne saboda zargin rashin biyayya ga kotu da ake yi mata. Kazalika, shugabannin jam'iyyar sun zargi Binani da haddasa ɓangaranci da rarraban kan mambobin jam'iyyar. Wannan na zuwa ne yayin da ya rage 'yan kwanaki kafin zaɓen gwamnoni a faɗin ƙasa. Ga…
Read More
Gangamin zaɓen 2023: APC ta bayyana gamsuwarta da goyon bayan al’ummar Jihar Yobe

Gangamin zaɓen 2023: APC ta bayyana gamsuwarta da goyon bayan al’ummar Jihar Yobe

Daga MUHAMMAD AL-AMEEN a Damaturu Shugaban Jam'iyyar APC na Jihar Yobe, Alhaji Muhammed Gadaka ya nemi haɗin kan dukkan magoya bayan Jam'iyyar APC a Yobe ta Kudu domin samun nasarar babban zaɓe mai zuwa na 2023. Shugaban Jam’iyyar ya yi wannan kiran ne a lokacin da yake jawabi a yaƙin neman zaɓen da Jam’iyyar APC ta gudanar a shiyya ta biyu (Zone B), a filin wasa na Dabo Aliyu da ke ƙaramar hukumar Potiskum a Jihar Yobe. Gadaka ya bayyana cewa, sai ta hanyar cikakken haɗin kai da goyon bayan al’ummar yankin ne Jam’iyyar APC za ta samu nasarar lashe…
Read More
Har yanzu CBN bai sakar wa INEC kuɗaɗe ba – Kwamishina

Har yanzu CBN bai sakar wa INEC kuɗaɗe ba – Kwamishina

Daga BASHIR ISAH Yayin da ya rage kwanaki kaɗan kafin zaɓen 2023, har yanzu Babban Bankin Nijeriya (CBN) bai sakar wa Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), kuɗaɗen da take buƙata domin tura kayayyakin zaɓe zuwa sassan ƙasa ba. A makon jiya Shugaban INEC na ƙasa, Farfesa Mahmood Yakubu, ya gana da Gwamnan CBN, Godwin Emefiele, inda suka tattauna yiwuwar bai INEC sabbin kuɗin da za ta yi amfani da shi wajen tura kayan zaɓe zuwa sassa. Inda a nan Emefiele ya bai wa INEC tabbacin ba zai bari a yi wa CBN kallon ana amfani da shi wajen yi wa…
Read More
Jerin mazaɓu 240 da INEC ta ce ba za a gudanar da zaɓe a cikinsu ba

Jerin mazaɓu 240 da INEC ta ce ba za a gudanar da zaɓe a cikinsu ba

Daga WAKILINMU Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), ta fitar da jerin sunayen mazaɓun da ta ce zaɓe ba zai gudana a cikinsu ba saboda rashin rijistar masu kaɗa ƙuri'a. Tun da fari, Shugaban INEC na Ƙasa, Mahmood Yakubu, ya bayyana a ranar Litinin cewa mazaɓun da lamarin ya shafa ba su da mutum ko guda da aka yi wa rijistar zaɓe a ƙarƙashinsu. A cewarsa, baki ɗaya mazaɓu 176,606 ake da su a faɗin ƙasa. Ya ƙara da cewa, waɗanda aka sauya wa mazaɓa za su samu saƙon tes ta waya mai ɗauke da bayanin mazaɓar da aka tura mutum…
Read More
Dalilin soke taron Atiku a Ribas – PDP

Dalilin soke taron Atiku a Ribas – PDP

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Shugaban Ƙasa na Jam’iyyar PDP a Jihar Ribas, ya ce an soke gangamin kamfe na Atiku Abubakar da aka shirya gudanarwa a Fatakwal don kauce wa asarar rayuka. Shugaban Kwamitin a Jihar Ribas, Sanata Lee Maeba ne ya bayyana haka a taron manema labarai da ya shirya ranar Litinin a Fatakwal, babban birnin jihar. Maeba ya ce an kai wa mambobin PDP da magoya bayan Atiku hare-hare a tsakanin watanni ukun da suka gabata a jihar. Kazalika, ya yi zargin Gwamnatin Ribas ta rufe harkokin kasuwancin wasu jiga-jigan mambobin jam’iyyar masu mara…
Read More
2023: Babu zaɓe a rumfunan zaɓe 240 – Yakubu

2023: Babu zaɓe a rumfunan zaɓe 240 – Yakubu

Daga BASHIR ISAH Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), ta ce zaɓe ba zai gudana ba a wasu rumfunan zaɓe 240 a faɗin ƙasa a zaɓe mai zuwa. Shugaban INEC na Ƙasa, Farfesa Mahmood Yakubu ne ya bayyana haka a wajen ganawarsu da jam'yyun siyasa a ranar Litinin. A cewar Yakubu, hakan ya faru ne saboda babu wanda ya zaɓi ya kaɗa kuri'a a rumfunan zaɓen da lamarin ya shafa. Wannan na zuwa ne yayin da ya rage kwanaki 12 kafin baban zaɓen 2023. A cewar Yakubu babu wanda ya nuna sha'awar kaɗa ƙuri'a a rumfanar yayin rijistar zaɓen da aka…
Read More
Gwamnatin Yobe ta ƙaryata kai wa jiga-jigan APC hari a wajen taro

Gwamnatin Yobe ta ƙaryata kai wa jiga-jigan APC hari a wajen taro

Daga WAKILINMU Gwamnatin Jihar Yobe, ta ƙaryata labarin da aka yaɗa a wasu kafafen yaɗa labarai cewa an yi wa gangamin yaƙin neman zaɓen Jam'iyyar APC ruwan duwatsu a Ƙaramar Hukumar Gashua da ke jihar. Darakta Janar na yaɗa labarai ga Gwamnan Yobe, Mamman Mohammed, ya ƙaryata faruwar haka, tare da cewa babu ƙamshin gaskiya a cikin lamarin. “Gangamin ya samu dubban mahalarta wanda ba taɓa ganin irinsa ba a tarihin siyasar garin Gashua. "Taron ya yi kyakkyawar tarba ga Shugaban Majalisar Dattawa, Ahmed Lawan, Gwamna Buni da mambobin Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓe. “Gwamna Buni ya ratsa taron zuwa kan…
Read More
Zaɓen 2023: Aski ya zo gaban goshi!

Zaɓen 2023: Aski ya zo gaban goshi!

Daga NASIRU ADAMU EL-HIKAYA Azancin zancen Hausawa na cewa aski in ya zo gaban goshi ya fi zafi duk da ba lalle kowa ya kan ji zafi don askin da a ke yi ma sa ya zo goshi ba. Gaskiya ma hakan ya danganta ga wanzamin da ya ke askin. Idan an samu goni ya jika sabulu da ɗan ruwa mai sanya ya shafa ya murza aska sai askin ya yi sanyi kuma har ma a riƙa hira tsakanin wanzamin da wanda a ke yi wa askin. Shin wannan zaɓen ya na zafi ko ba shi da shi a zahiri…
Read More