19
Feb
Daga ABUBAKAR A. BOLARI a Gombe Wata 'yar siyasa a Jihar Gombe kuma jigo a tafiyar yaqin neman zaven ɗan takarar gwamnan jihar a Jam'iyyar PDP Muhammad Jibrin Barde, Hajiya Uwani Hamsal, ta ce 'yan Nijeriya sun gamsu da ajandoji 5 da ɗan takarar shugabancin Nijeriya Atiku Abubakar, ya zayyana. Hajiya Uwani Hamsal, ta ce ajandoji 5 da suka ƙunshi, inganta tsaro da farfaɗo da harkar noma, da ilimi da kasuwancin da kuma samar da ayyukan yi ga 'yan Nijeriya da ma su ne abinda suka daɗe suna ci wa 'yan Nijeriya tuwo a ƙwarya. Hajiya Uwani, ta bayyana hakan…