09
Sep
Ana yunƙurin fitar da ofishin mataimakin daga fadar gwamnati Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Rikicin da ke tsakanin Gwamnan Jihar Edo, Godwin Obaseki da mataimakinsa, Philip Shaibu na ci gaba da ruruwa yayin da ake shirin mayar da mataimakinsa wani gini da ke wajen gidan gwamnati. Ginin da ke lamba 7, Dennis Osadebey Avenue, kusa da gidan gwamnati, wanda shine ofishin hukumar saye da sayarwa ta jihar Edo, an gyara shi domin ya zama ofishin mataimakin. Tsohon gwamnan jihar, Adams Oshiomhole ne ya qaddamar da ginin a ranar 16 ga watan Disamba, 2014. Sai dai kuma da aka tuntuɓi…
