17
Feb
Daga MUHAMMAD AL-AMEEN a Damaturu Shugaban Jam'iyyar APC na Jihar Yobe, Alhaji Muhammed Gadaka ya nemi haɗin kan dukkan magoya bayan Jam'iyyar APC a Yobe ta Kudu domin samun nasarar babban zaɓe mai zuwa na 2023. Shugaban Jam’iyyar ya yi wannan kiran ne a lokacin da yake jawabi a yaƙin neman zaɓen da Jam’iyyar APC ta gudanar a shiyya ta biyu (Zone B), a filin wasa na Dabo Aliyu da ke ƙaramar hukumar Potiskum a Jihar Yobe. Gadaka ya bayyana cewa, sai ta hanyar cikakken haɗin kai da goyon bayan al’ummar yankin ne Jam’iyyar APC za ta samu nasarar lashe…