10
Aug
Daga BASHIR ISAH Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓe mai zamanta a Kano, ta tsige ɗan Majalisar Wakilai na ƙasa mai wakiltar Mazaɓar Tarauni, Honorabul Muktar Umar Yarima na Jam'iyyar NNPP bayan da ta same shi da laifin amfani da takardar bogi. Kotun ta ce takardar shaidar kammala makarantar firamare da Yarima ya gabatar ta jabu ce kamar yadda ta bayyana a zaman shari'ar da ta yi a ranar Alhamis. Don haka Kotun ta buƙaci hukumar zaɓe INEC da ta bayyana ɗan takarar Jam'iyyar APC a mazaɓar, Honorabul Hafizu Ibrahim Kawu, a matsayin wanda ya lashe zaɓen sannan ta miƙa masa shaidar…
