Siyasa

Adamu ya yi murabus daga shugabancin Jam’iyyar APC

Adamu ya yi murabus daga shugabancin Jam’iyyar APC

Daga BASHIR ISAH Sbugaban Jam'iyyar APC na Ƙasa, Sanata Abdullahi Adamu, ya miƙa wasiƙar yin murabus daga kujerarsa ta shugabancin jam'iyyar kamar yadda Jaridar News Point Nigeria ta rawaito. Majiyar News Point Nigeria ta bayya cewar, Sanata Adamu wanda ya zama shugaban APC a watan Maris, 2022, ya miƙa wasiƙar murabus daga muƙaminsa ga Fadar Shugaban Ƙasa gabanin dawowar Shugaba Bola Ahmed Tinubu daga taron Ƙungiyar Ƙasashen Afirka (AU) da ya halarta a ƙasar Kenya. Majiyar jaridar ta ce, Adamu ya aike da wasiƙar tasa ce ga Shugaban Ma'aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Femi Gbajabiamila, da misalin ƙarfe 4 na yammacin…
Read More
Ɗan takarar Gwamna ya je Kotun Sauraron Ƙararrakin Zaɓe da shaidu 8,000

Ɗan takarar Gwamna ya je Kotun Sauraron Ƙararrakin Zaɓe da shaidu 8,000

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Mutumin da ya yi wa Jam’iyyar PDP takara a zaɓen Gwamnan Jihar Ogun na 2023, Ladi Adebutu, a ranar Talata ya isa kotun sauraron kararrakin zaɓen jihar da shaidu har guda 8,000. Ɗan takarar dai na ƙalubalantar nasarar da Dapo Abiodun ya samu a zaɓen Gwamnan Jihar da aka gudanar ranar 18 ga watan Maris ɗin da ya gabata. A kwafin ƙarar tasa mai lamba EPT/OG/GOV/03/2023, ɗan takarar ya ce ya shigar da ƙarar ce saboda yana zargin ba a bi Dokar Zaɓe ta Nijeriya ba a yayin zaɓen. Alqalai uku ne dai suke…
Read More
APC ta nesanta kanta da batun manyan muƙaman da aka naɗa a Majalisar Tarayya

APC ta nesanta kanta da batun manyan muƙaman da aka naɗa a Majalisar Tarayya

Daga BASHIR ISAH Shugaban Jam'iyyar APC na Ƙasa, Sanata Abdullahi Adamu, ya nesanta jam'iyyar da batun manyan muƙaman da aka naɗa a Majalisar Tarayya kamar yadda shugabancin majalisar dattawa da ta wakilai suka sanar a ranar Talata. Yayin taro da Kwamitin Gudanawar na Ƙasa na jam'iyyar da ƙungiyar gwamnonin APC a Abuja, Adamu ya ce Majalisar Tarayya ta saɓa ƙa'ida wajen sanar da manyan jami'an da aka naɗa ba tare da sanin jam'iyyar ba kamar yadda tashar AIT ta rawaito. A zaman da majalisun suka yi a ranar Talata aka jiyo Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio da Shugaban Majalisar…
Read More
An yi naɗe-naɗen manyan muƙamai a Majalisar Tarayya

An yi naɗe-naɗen manyan muƙamai a Majalisar Tarayya

Daga BASHIR ISAH Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio da Shugaban Majalisar Wakilai, Tajudeen Abbas, sun yi naɗe-naɗe na manyan muƙamai a majalisar tarayya. A yayin zaman majalisun a ranar Talata Akpabio da Abbas suka sanar da naɗe-naɗen sabbin manyan muƙaman da aka yi. A Majalisar Dattawa, Akpabio ya ambaci Opeyemi Bamidele a matsayin Shugaban Masu Rinjaye, David Umahi a matsayin Mataimakin Shugaban Masu Rinjaye; Mohammed Ali Ndume a matsayin Mai Tsawatarwa na Masu Rinjaye, sai Lola Ashiru a matsayin Mataimakin Mai Tsawatarwa na Masu rinjaye. Yayin da a Majalisar Wakilai kuwa, Abbas ya ambaci Julius Ihonvbere daga Edo a…
Read More
Rahoton EU: Atiku da Obi sun yi ca a kan Tinubu

Rahoton EU: Atiku da Obi sun yi ca a kan Tinubu

Daga BASHIR ISAH 'Yan takarar shugaban ƙasa, Atiku Abubakar na Jam'iyyar PDP da Peter Obi na Jam'iyyar Labour a zaɓen 2023 da ya gabata, sun yi ca a kan Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, na ƙin yarda da rahoton ƙarshe da Ƙungiyar Tarayyar Turai (EU) ta fitar kan zaɓen shugaban ƙasa da ya gudana a ranar 25 ga Fabrairun da ya gabata. A ranar Talata, 27 ga Yuni, EU ta miƙa rahoton nata game da zaɓen a Abuja. Babban jami'in sanya ido, Barry Andrews, ya ce rahoton ya samo asali ne daga nazarin bin ƙa’idojin da Nijeriya ta ɗauka na…
Read More
Rigimar Majalisar Dokokin Nasarawa: Mambobin ɓangaren Ogazi na canja sheƙa zuwa ɓangaren Balarabe

Rigimar Majalisar Dokokin Nasarawa: Mambobin ɓangaren Ogazi na canja sheƙa zuwa ɓangaren Balarabe

Daga JOHN D. WADA a Lafiya Idan ba a manta ba a 'yan kwanakin nan ne Majalisar Dokokin Jihar Nasarawa ta tsunduma cikin rikici da ya ƙi ci ya ƙi cinyewa jim kaɗan bayan zaɓen kujeral Kakakin Majalisar wanda aka so a gudanar a lokacin amma bai yu ba, inda a ƙarshe aka samu ɓangarori 2 tsakanin mambobin majalisar inda wasu ke goyon bayan tsohon kakakin majalisar, Ibrahim Balarabe Abdullahi wanda ke neman zarcewa a kujerar, yayin da wasu kuma ke tare da Ogah Ogazi da shi ma yake neman hawa kujera. Kodayake a lokacin ma fi yawan 'yan majalisar…
Read More
Shari’ar nasarar Tinubu: Lauyoyin Tinubu sun zargi Manhajar Amazon da haifar da matsalar da INEC ta samu da Rumbun IReV

Shari’ar nasarar Tinubu: Lauyoyin Tinubu sun zargi Manhajar Amazon da haifar da matsalar da INEC ta samu da Rumbun IReV

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaba Bola Tinubu ta bakin lauyoyinsa, ya shaida wa Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓen Shugaban Ƙasa cewa Rumbun Adana Bayanai a Yanar Gizo na Amazon, ba shi da garanti, ya na iya samun matsala. Sai dai kuma wani ƙwararren injinijya na Amazon ya ƙaryata lauyoyin Tinubu ɗin. AWS Incorporated a ƙarƙashin Amazon ne suka buɗe wa INEC Rumbun Manhajar Tattara Sakamakon Zaɓe ta IReV, a lokacin zaven 2023. Atiku da Peter Obi duk sun ƙalubalaci ƙin watsa sakamakon zaɓe, wanda su ka ce ba a watsa a IReV ba, kamar yadda INEC ta yi alƙawarin…
Read More
A mayar da tsohon mataimakin gwamnan Zamfara Mahdi da aka tsige kujerarsa – Kotu

A mayar da tsohon mataimakin gwamnan Zamfara Mahdi da aka tsige kujerarsa – Kotu

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Babbar Kotun Tarayya da ke zamanta a Abuja ta bada umarnin mayar da tsohon Mataimakin Gwamnan Jihar Zamfara wanda aka tsige, wato Mahadi Aliyu Gusau kan kujerarsa. Mahadi dai shi ne Mataimakin Gwamna zamanin mulkin tsohon Gwamna Bello Matawalle, wanda aka tsige saboda ya ƙi bin shi Jam’iyyar APC daga PDP. Mahadi da PDP ne suka shigar da ƙarar suna ƙalubalantar tsige shi da Majalisar Dokokin Jihar ta yi a watan Fabrairun 2022. Da yake yanke hukunci a ranar Laraba, Alƙalin kotun, Mai Shari’a Inyang ya ce matakin da tsohon Gwamna Matawalle da kwamitin…
Read More
Gwamna Bala ya zama shugaban gwamnonin PDP

Gwamna Bala ya zama shugaban gwamnonin PDP

Daga BASHIR ISAH An zaɓi Gwamna Bala Mohammed na Jihar Bauchi a matsayin Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin PDP, yayin da Gwamnan Ribas, Siminalayi Fubara, ya zama mataimakin shugaban ƙungiyar. An zaɓi Mohammed da Fubara ne a wajen taron bitar da PDP ta shirya wa zaɓaɓɓun jami'anta wanda ya gudana a Fadar Gwamnatin Jihar Bauchi a ranar Asabar. Gwamna Mohammed ya maye gurbin gwamnan Oyo ne, wato Seyi Makinde, wanda shi ma ya halarci taron na yini guda. Da yake jawabi a wajen taron, Shugaban riƙo na ƙasa na Jam'iyyar PDP, Umar Damagum, ya nuna wa jagororin buƙatar da ke akwai a…
Read More
Jam’iyyar Labour da Peter Obi sun kasa ci gaba da gabatar da bayanai a kotu

Jam’iyyar Labour da Peter Obi sun kasa ci gaba da gabatar da bayanai a kotu

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Jam'iyyar hamayya ta Labour da ɗan takararta Peter Obi sun kasa ci gaba da bayar da bahasi a ƙarar da suka shigar a gaban kotun zaɓen shugaban ƙasa, a ranar Laraba. Kotun ta ba su ƙarfe 9 na safe a ranar Laraba, domin ci gaba da gabatar da bayanansu a gabanta ta hanyar kawo ƙarin shedu da takardu, inda aka ba su sa'a huɗu su yi hakan. Sai dai yayin da kotun ta zauna, lauyan masu ƙarar, Awa Kalu (SAN) ya gaya wa alƙali cewa sun shirya gabatar da wasu takardu, amma kuma suka…
Read More