Siyasa

Abin da Kwankwaso da Tinubu suka tattauna a ƙasar waje

Abin da Kwankwaso da Tinubu suka tattauna a ƙasar waje

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaban Ƙasa mai jiran gado, Bola Tinubu ya yi wata ganawar sirri da ɗan takarar shugaban kasa na Jam’iyyar NNPP, Sanata Rabiu Kwankwaso a ƙasar Faransa. Wata majiya mai tushe ta ce Tinubu ya yi wa Kwankwaso tayin tafiya tare da shi a sabuwar gwamnati da kuma duba yiwuwar sulhu tsakaninsa da Gwamnan Kano mai barin gado, Abdullahi Ganduje. A ranar Litinin, mako biyu kafin Tinubu ya karɓi rantsuwar fara aiki, suka shafe sama da awa huɗu suna ganawar sirrin da Kwankwaso a birnin Paris na ƙasar Faransa. Majiyarmu ta ce a yayin ganawar,…
Read More
Muna da kyakkyawar fata Atiku Abubakar zai nasarar zama Shugaban Ƙasa a kotu – Mai-Nasiha

Muna da kyakkyawar fata Atiku Abubakar zai nasarar zama Shugaban Ƙasa a kotu – Mai-Nasiha

Daga IBRAHIM MUHAMMAD a Kano Wani ɗan Jam'iyyar PDP a Jihar Kano, Alhaji Salman Mai Nasiha ya bayyana cewa a yadda suke ganin ana gudanar da shari'ar ƙorafin zaven Shugaban Ƙasa a Babbar Kotun Abuja, suna kyautata zaton Atiku Abubakar zai yi nasara. Mai-Nasiha ya bayyana hakan ne yayin da yake hira da 'yan jarida, inda kuma ya yi nuni da cewa al'ummar ƙasar nan sun yi wa Buhari kyakkyawan zato a mulkinsa za su samu saulin rayuwa da walwala amma sai ga shi ya jefa mutane a mafi ƙuncin rayuwa da ba a tava tsammani ba. Ya ƙara da…
Read More
Ɗan takarar da Gbajabiamila ke son ya gaje shi barazana ce ga dimokuraɗiyyar Nijeriya – Hon. Nalaraba

Ɗan takarar da Gbajabiamila ke son ya gaje shi barazana ce ga dimokuraɗiyyar Nijeriya – Hon. Nalaraba

Daga SANI AHMAD GIWA Honorabul Abubakar Hassan Nalaraba ya bayyana cewa shirin da ake zargin Kakakin Majalisa, Femi Gbajabiamila na yi na ɗora Hon. Abbas Tajuddeen a matsayin wanda zai gaje shi a Majalisar Wakilai ta 10 yana da haɗari ga dimokuraɗiyyar Nijeriya. Ya bayyana hakan ne a wani taron manema labarai da ya kira a Abuja, kan zargin dambarwa da ake yi wa ɗan takara a tsarin dimukoraɗiyya, inda ya bayyana hakan a matsayin savani, rashin bin tsarin dimokuraɗiyya, mulkin kama-karya da kuma babban hatsari ga dimokuraɗiyya, savanin ɗan takararsa, Honorabul Mukhtar Aliyu Betara da ba shi da tsara.…
Read More
Ba ni ba sake fitowa takara bayan na kammala wa’adina na biyu, inji Gwamna Abdullahi Sule

Ba ni ba sake fitowa takara bayan na kammala wa’adina na biyu, inji Gwamna Abdullahi Sule

Daga JOHN D. WADA a Lafiya Gwamnan Jihar Nasarawa Injiniya Abdullahi Sule, ya ce da zarar ya kammala wa’adinsa na biyu a matsayin gwamnan jihar, ba zai sake fitowa takarar kujerar siyasa ba har ƙarshen rayuwarsa. Gwamnan ya sanar da haka ne a lokacin da yake karɓar baƙuncin ‘ya’yan ƙungiyar masu aiko da rahoto wato Correspondents Chapel a turance na ƙasa reshen jihar ta Nasarawa waɗanda suka kai masa ziyarar taya shi murnar bikin ƙaramar Sallah da aka gudanar kwanan nan a gidansa dake garin Gudi dake yankin Ƙaramar Hukumar Akwanga a jihar. Ya ce a yanzu Alhamdu lillah da…
Read More
Sauraren Ƙararrakin Zaɓe: Atiku Abubakar ya halarci zaman kotu

Sauraren Ƙararrakin Zaɓe: Atiku Abubakar ya halarci zaman kotu

Ɗan takarar Shugaban Ƙasa ƙarƙashin Jam'iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya halarci zaman shari'ar da Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓe ki yi a Abuja a wannan Alhamis ɗin. Atiku ya halarci Kotun ne domin jin yadda za ta kaya kan ƙarar da ya shigar inda yake ƙalubalantar nasarar da ɗan takarar shugabancin ƙasa na Jam'iyyar APC, Bola Tinubu, ya samu a babban zaɓen da ya gudana. Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasar shi ne ya zo na biyu a babban zaɓen da aka yi ran 25 ga Fabrairu, yayin da Peter Obi na Jam'iyyar Labour ya zo na uku. Atiku yana zargin an tafka…
Read More
Da Ɗumi-ɗumi: Kotun Ƙoli ta tabbatar da Adeleke a matsayin Gwamnan Osun

Da Ɗumi-ɗumi: Kotun Ƙoli ta tabbatar da Adeleke a matsayin Gwamnan Osun

Kotun Ƙoli ta yi watsi da ƙarar da Adegboyega Oyetola na Jam'iyyar APC ya ɗaukaka inda yake ƙalubalantar nasarar da Ademola Adeleke na Jam'iyyar PDP ya samu a matsayin Gwamnan Jihar Osun. Da yake karanto hukuncin yayin zaman kotun a ranar Talata, Mai Shari'a Emmanuel Agim ya tabbatar da hukuncin da Kotun Ɗaukaka Ƙara ta yanke na cewa Adeleke shi ne wanda ya yi nasara a zaɓen na Osun. Kotun Ƙolin ta ce mai ƙara ya gaza gabatar wa kotun gamsassun hujjoji kan zargin da ya yi cewa an zuba ƙuri'a wuce kima a zaɓen gwamnan jihar Osun da ya…
Read More
APC ta yi ra’ayin Akpabio da Barau su jaigoranci Majalisar Ƙasa

APC ta yi ra’ayin Akpabio da Barau su jaigoranci Majalisar Ƙasa

Kwamitin Gudanarwa na Ƙasa na Jam'iyyar APC (NWC) ya sannar da bin tsarin karɓa-karɓa dangane da shugabancin Majalisar Taraya zubi na 10. A cewar sanarwar da jam'iyyar ta fitar a ranar Litinin ta bakin Sakataren Yaɗa Labarai na Ƙasa, Felix Morka, tsarin karɓa-karɓar da jami'yyar ta shirya yin amfani da shi ya ƙunshi: Shugaban Majalisar Dattawa - Kudu maso Kudu - Sanata Godswill Akpabio (Akwa Ibom), Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa – Arewa maso Yamma - Sanata Barau Jubrin (Kano). Sauran su ne; Shugaban Majalisar Wakilai, Arewa maso Yamma – Hon. Abass Tajudeen (Kaduna), Mataimakin Shugaban Majalisar Wakilai Deputy Kudu maso…
Read More
Nasarar da Lawan Dare ya samu a Gwamnan Zamfara ba tirsasa wa al’umma aka yi ba – Mai-Nasiha

Nasarar da Lawan Dare ya samu a Gwamnan Zamfara ba tirsasa wa al’umma aka yi ba – Mai-Nasiha

Daga IBRAHIM MUHAMMAD a Kano An ƙalubalanci maganar da Gwamnan Jihar Zamfara ya yi na zargin cewa an yi amfani da wasu jami'an tsaro, sojoji da 'yan sanda sun tursasa wa mutane, su zaɓi Jam'iyyar PDP ba jam'iyyarsa ta APC ba, da cewa wannan magana da ya yi ba haka ba ne, kuma babu ƙamshin gaskiya a cikinta.  Jigo a Jam'iyyar PDP a Jihar Kano kuma masoyi, hadimi ga zaɓaɓɓen gwamnan jihar Zamfara Alhaji Dauda Lawan Dare, Malam Salmanu Mai Nasiha ne ya yi wannan ƙalubalen da yake mai da martani ga maganganun Gwamnan Zamfara Matawalle da ya ke zantawa…
Read More
‘Yan sanda sun cika hannu da korarren Kwamishinan Zaɓen Adamawa, Yunusa-Ari

‘Yan sanda sun cika hannu da korarren Kwamishinan Zaɓen Adamawa, Yunusa-Ari

'Yan sanda sun damƙe korarren Kwamishinan Zaɓe na Jihar Adamawa, Hudu Yunusa-Ari, kan abin da ya aikata yayain zaɓen gwamna a jihar. Kakakin 'yan sanda, Muyiwa Adejobi, ya bayyana a cikin sanarwar da ya fitar ranar Talata cewa, yanzu haka 'yan sanda na tsare da Yunusa-Ari. Sanarwar ta ce 'yan sanda sun cika hannu da Arin ne a Abuja, inda yake ci gaba da amsa tambaya kan dalilin da ya sa ya yi riga malam masallaci wajen bayyana sakamakon zaɓe alhali ana tsaka da tattara sakamakon zaɓen yayin zaɓen cike giɓi na gwamnan jihar da ya gudana kwanan baya. Ari…
Read More
Mun zo aikin ceto ne, cewar Zaɓaɓɓen Gwamnan Zamfara

Mun zo aikin ceto ne, cewar Zaɓaɓɓen Gwamnan Zamfara

Zaɓaɓɓen Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, a'ya ƙaddamar da kwamitin karɓar mulki a ranar Talata a Gusau, babban birnin jihar. Yayin ƙaddamar da kwamitin mai membobi 60, Dauda Lawal ya jaddada cewa ya zo aikin ceto ne tare da sake gina Jihar Zamfara. Sanarwar da ofishin zaɓaɓɓen gwamnan ya fitar mai ɗauke da sa hannun Sulaiman Bala Idris ta nunar cewa, an kafa kwamitin karɓar mulkin ne a ƙarƙashin jagorancin tsohon Sufeto Janar na ‘yan sanda, M.D Abubakar. Da yake jawabi a wajen ƙaddamar da kwamitin, mai girma Dauda Lawal, ya ce nauyin da ya rataya a kan kwamitin shi…
Read More