26
Feb
Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau. Wata mata mai juna-biyu mai suna Shamsiya Ibrahim ta yanke jiki ta faɗi matacciya a yayin da take jiran layin kaɗa ƙuri'a yayin zaɓen Shugaban Ƙasa da na 'yan Majalisar Tarayya. Wannan al'amari ya auku ne ranar Asabar a yankin ƙaramar hukumar Tsafe da ke Jihar. Blueprint Manhaja ta tattaro cewa bayan da matar ta yanke jiki ta faɗi, an garzaya da ita Babban Asibitin Tsafe inda aka tabbatar da rasuwarta. Shamsiya ta yi tattaki ne daga yankin Kotorkoshi da ke Ƙaramar Hukumar Bunguɗu zuwa garin Tsafe mai nisan kimanin kilomita 50 don kaɗa ƙuri’arta.…