Siyasa

Shugabancin Bayelsa: Kotu ta soke cancantar shiga takarar ɗan takarar APC, Sylva

Shugabancin Bayelsa: Kotu ta soke cancantar shiga takarar ɗan takarar APC, Sylva

Babbar Kotun Tarayya mai zamanta a Abuja, ta soke cancantar shiga takara ta ɗan takarar jam'iyyar APC, Cif Timipre Sylva, a zaɓen gwamnan jihar Bayelsa mai zuwa. A ranar Litinin kotun a ƙarƙashin jagorancin Mai Shari'a Donatus Okorowo, ta yanke wannan hukuncin. Ya zuwa ranar 11 ga watan Nuwamban 2023 ne ake sa ran gudanar da zaɓen gwamna a jihar ta Bayelsa. Alƙalin ya ce tun da an taɓa rantsar da Sylva sau biyu a matsayin gwamnan jihar kuma ya yi mulki na tsawon shekara biyar, sake shiga takarar gwamna a jihar hakan ya saɓa wa Kundin Tsarin Mulki na…
Read More
Kotu ta tabbatar da zaɓen Gwamna Idris na Kebbi

Kotu ta tabbatar da zaɓen Gwamna Idris na Kebbi

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Kotun Sauraron Ƙararrakin Zaɓe ta Jihar Kebbi, ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a Ofemai Ofem, ta yi watsi da ƙarar da jam’iyyar adawa ta PDP ta shigar tana ƙalubalantar nasarar Gwamna Nasir Idris. Da yake yanke hukuncin a gaban lauyoyi da jiga-jigan jam’iyyar APC, tun da farko alƙalin ya yi fatali da zarge-zargen da ake yi wa mataimakin gwamnan jihar Umar Tafida, bayan da ya miƙa takardar shaidar makarantar da ya halarta a matsayin shaida. A game da kura-kuran zaɓe, kotun ta ce kimanin shaidu 17 daga hukumar zaɓe ta INEC sun tabbatar da cewa zaɓen ba shi…
Read More
An tsige Kakakin Majalisar Wakilan Amurka, Kevin McCarthy

An tsige Kakakin Majalisar Wakilan Amurka, Kevin McCarthy

A ranar Talata 'yan Majalisar Wakilan ƙasar Amurka suka tsige Kakakin majalisar, Kevin McCarthy, bayan kaɗa ƙuri'ar jin ra'ayi. Wannan al'amari wanda tarihin siyasar ƙasar ba zai mance da shi ba, ya jefa 'yan Jam'iyyar Republican a majalisar cikin ruɗani. Da wannan mataki da 'yan majalisar suka ɗauka, yanzu ya zama wajibi su zaɓi wanda zai maye gurbin McCarthy. Sai dai ya zuwa haɗa wannan rahoto, babu cikakken bayani kan wanda za a zaɓa a matsayin sabon kakakin Majalisar. Kodayake dai 'yan majalisar sun naɗa Patrick McHenry na Carolina ta Arewa a matsayin muƙaddashin kakakin Majalisar ya zuwa lokacin da…
Read More
Da Ɗumi-ɗumi: Kotu ta ƙwace kujerar Gwamnan Nasarawa daga hannun APC ta miƙa wa PDP

Da Ɗumi-ɗumi: Kotu ta ƙwace kujerar Gwamnan Nasarawa daga hannun APC ta miƙa wa PDP

Kotun Sauraren Ƙorafe-ƙorafen Zaɓen Gwamnan Jihar Nasarawa, ta tsige Injiniya Abdullahi Sule a matsayin Gwamnan Jihar Nasarawa. Biyu daga cikin alƙalan kotun su uku ƙarƙashin jagorancin Mai Shari'a Ezekiel Ajayi, sun bayyana ɗan takarar Jam'iyyar PDP, David Umbugadu a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamnan da ya gudana a wannan shekarar da ake ciki. Ya zuwa haɗa wannan labarin alƙali na, Jastis Ibrahim Mashi, bai kai ga bayyana nasa hukuncin ba.
Read More
Shin waye bai taɓa sauya sheƙa ba?

Shin waye bai taɓa sauya sheƙa ba?

Tare da NASIRU ADAMU EL-HIKAYA Sheƙa dai da duk wanda ya fahimci sunan na nufin ‘Gidan Tsustsu” da ya kan gina ko sassarƙafa da kan sa cikin baiwar da Allah ya yi ma sa. Haƙiƙa tsuntsaye na da basirar gasken gaske don yadda su kan saka sheƙar nan su kaɗai. Za ka ga wasu tsuntsayen na tafiya wani waje su na ɗauko kayan haɗa sheƙa ɗaya bayan ɗaya su na sagalawa har su gama. Kwanan nan naga wani hoto mai ban tausayi da ke nuna ’ya’yan wata tsuntsuwa sun mutu a cikin sheƙa sai a ka rubuta ba mamaki an…
Read More
An shiga ruɗani game da hukuncin kotu kan shari’ar zaɓen Gwamnan Kaduna

An shiga ruɗani game da hukuncin kotu kan shari’ar zaɓen Gwamnan Kaduna

Jama'a sun shiga halin ruɗani game da shari'ar zaɓen gwamna a jihar Kaduna. Hakan ya faru ne bayan da wani rahoto ya nuna Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓe na Gwamnan Jihar ta ayyana zaɓen a matsayin wanda bai kammala ba. Bayan kimanin awa guda da fitan rahoton, sai aka sake ganin wani rahoto na daban na cewa, kotun ta tabbatar da nasarar da Gwamna Uba Sani ya samu a zaɓen wanda hakan ke nuni da shi ne zaɓaɓɓen gwamnan jihar. Da yake yi wa Jaridar News Point Nigeria ƙarin haske game da hukuncin ta waya, lauyan Gwamna Sani, Ibrahim H O…
Read More
Da Ɗumi-ɗumi: Kotu ta ayyana zaɓen gwamnan Kaduna ‘Inconclusive’

Da Ɗumi-ɗumi: Kotu ta ayyana zaɓen gwamnan Kaduna ‘Inconclusive’

Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓen Gwamnan Jihar Kaduna, ta ayyana zaɓen gwamnan jihar da ya gudana ran 18 ga Maris a matsayin wanda bai kammala ba, wato 'inconclusive.' Kotun ta ayyana hakan ne a zaman yanke hukunci kan shari'ar da ta yi a ranar Alhamis. Kotun, ƙarƙashin jagorancin Mai Shari'a Victor Oviawe ta bai wa Hukumar Zaɓe ta Ƙasa INEC, da ta gudanar da zaɓen cike giɓi a cikin kwana 90. Da wannan hukuncin, ana sa ran INEC ta sake shirya zaɓe a gundumomi bakwai a tsakanin ƙananan hukumomi huɗu kuma a rumfunan zaɓe 24 masu ɗauke da masu kaɗa ƙuri'a…
Read More
Shari’ar siyasar Kano: Inda jami’yyar NNPP mai mulki ta kuskure

Shari’ar siyasar Kano: Inda jami’yyar NNPP mai mulki ta kuskure

Daga ABDULAZIZ TIJJANI BAQO A matsayina na ɗan NNPC kuma ɗan kwankwasiyya cikakke, ga mahangata a game da hukuncin da kotu ta yanke a kan shari'ar da ake tafkawa a tsakanin jam'iyyarmu ta NNPP da kuma APC. Bayan karanta kes ɗinmu da APC daga farko zuwa ƙarshe, ba ni da wani haufi a kan cewa lauyoyinmu su suka yi mana illa a wannan kes din. Sun yi iya bakin ƙoƙarinsu. Amma kuskuren da suka yi wurin laƙantar doka ya jawo mana matsala. Kusan gabaɗaya kariyar da suka bayar ta dogara ne da roko kotu ta yi watsi da hujjojin da…
Read More
Da Ɗumi-ɗumi: Kotu ta tabbatar da Yahaya a matsayin zaɓaɓɓen Gwamnan Gombe

Da Ɗumi-ɗumi: Kotu ta tabbatar da Yahaya a matsayin zaɓaɓɓen Gwamnan Gombe

Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓen Gwamnan Jihar Gombe ta tabbatar da Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamnan jihar. Yayin zamanta a ranar Talata, kotun ta yi watsi da ƙarar da aka shigar inda ake ƙalubalantar nasarar lashe zaɓen da Yahaya ya yi. 'Yan takaran jam'iyyun hamayya a jihar, wato Jibrin Barde na PDP da Nafiu Bala na ADC, su ne suka shigar da ƙarar inda suka nuna rashin gamsuwarsu da sake zaɓen Inuwa Yahaya da Mataimakinsa, Manassah Daniel Jatau da aka yi a matsayin shugabannin jihar ƙarƙashin Jam'iyyar APC. Duka alƙalan kotun su uku, sun yi…
Read More
Shugabancin Legas: Gwamna Sanwo-Olu ya yi nasara a kotu

Shugabancin Legas: Gwamna Sanwo-Olu ya yi nasara a kotu

Kotun Sauraren Ƙorafe-ƙorafen Zaɓen Gwamna a Jihar Legas, ta tabbatar da Gwamna Babajide Sanwo-Olu a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamnan jihar. Da yake karanto hukuncin a madadin sauran alƙalan yayin zaman kotun a ranar Litinin, Mai Shari'a Mikail Abdullahi ya ce ƙarar da Jam'iyyar PDP da ɗan takararta, Olajide Adediran, suka shigar ba ta da daraja wanda hakan ne ya sa kotu ta kori ƙarar. Tuhumar da ake yi wa Gwamnan Sanwo-Olu ta haɗa da amfani da takardun bogi da kuma cewa jam'iyyarsu ta APC ba ta tsayar da shi da mataimakinsa takara bisa ƙa'ida ba. Bayan sauraren duka…
Read More