Siyasa

Tinubu ya naɗa sabbin kwamishinonin INEC na jihohi guda tara

Tinubu ya naɗa sabbin kwamishinonin INEC na jihohi guda tara

Daga BASHIR ISAH Shugaba Bola Tinubu ya amince da naɗin kwashinonin zaɓe na jihohi (RECs) guda tara ga Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) na wa'adin shekara biyar. Tinubu ya naɗa kwamishinonin zaɓen ne kafin daga bisani Majalisar Dattawa ta tabbatar da naɗin nasu. Bayanin naɗin na ƙunshe ne cikin sanarwar da mai magana da yawun Shugaban Ƙasa, Ajuri Ngelale, ya fitar a ranar Laraba. Sanarwar ta ce Tinubu ya yi naɗin ne bisa damar da Sashe na 154 (1) na Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya na 1999 wanda aka yi wa kwaskwarima, da Sashe na 6 na Dokar Zaɓe ta 2022…
Read More
Shugaban INEC ya gana da jam’iyyun siyasa gabanin zaɓen gwamnoni a jihohin Kogi, Bayelsa, Imo

Shugaban INEC ya gana da jam’iyyun siyasa gabanin zaɓen gwamnoni a jihohin Kogi, Bayelsa, Imo

Shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), Mahmood Yakubu, ya gana da shugabannin jam'iyyun siyasa a hedikwatar hukumar da ke Abuja a ranar Talata. Taron ɓangare na shirye-shiryen da INEC ke yi don gudanar da zaɓen gwamnoni a jihohin Kogi da Bayelsa da kuma Imo nan gaba kaɗan. Ana sa sa ran shugaban INEC ya yi wa jam'iyyun bayanin shirye-shiryen INEC kan zaɓuɓɓukan da kuma rawar da Jam'iyyun za su taka. Kazalika, taron wata dama ce ga jam'yyun da lamarin ya shafa su bayyana wa shugban INEC damuwarsu da sauran lamurran da suka yi la'akari da su gabanin zaɓen.
Read More
Jaruma Tonto Dikeh ta sauya sheƙa zuwa APC

Jaruma Tonto Dikeh ta sauya sheƙa zuwa APC

Jaruma a masana'antar Nollywood wadda ta tsunduma harkar siyasa, Tonto Dikeh, ta sauya sheƙa ta koma Jam'iyya mai mulki ta APC. Jarumar ta koma APC ne bayan da ta fice daga Jam'iyyar hamayya ta African Democratic Congress (ADC). Jarumar ta yi takarar mataimakin gwamna ƙarƙashin ADC yayin zaɓen 2023 a Jihar Ribas. A wannan Litinin ɗin ake sa ran Shugabar Matan APC ta Ƙasa, Dr Mary Alile, za ta karɓi Tonto Dikeh a Sakatariyar APC da ke Abuja da misalin ƙarfe 3 na rana. A shekarun baya-bayan nan, an ga yadda jaruman fina-finai na Arewaci da Kudancin Nijeriya suka ba…
Read More
Kotun Ƙoli ta yi watsi da ƙarar APM kan ƙalubalantar nasarar Tinubu

Kotun Ƙoli ta yi watsi da ƙarar APM kan ƙalubalantar nasarar Tinubu

Kotun Ƙoli ta yi watsi da ƙarar da Jam'iyyar Allied People’s Movement (APM) ta shigar inda take ƙalubalantar nasarar da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya samu a zaɓen 2023. A ranar Litinin Kotun ta yi watsi da ƙarar bayan da mai ƙarar ta janye ƙarar da ta ɗaukaka. APM ta ɗaukaka ƙarar ne don ƙalubalantar sakamakon zaɓen shugaban ƙasa na 2023 wanda Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta bayyana Tinubu a matsayin wanda ya lashe zaɓen. Tun da fari, Jam'iyyar ta AMP ta nuna rashin gamsuwarta da hukuncin Kotun Sauraron Ƙararrakin Zaɓen Shugaban Ƙasa ta yanke wanda hakan ya…
Read More
Mutum uku ne suka ɗora Tinubu

Mutum uku ne suka ɗora Tinubu

Daga BELLO MUHAMMAD SHARAƊA Ranar 25 ga watan Fabrairu 2023, jama'ar ƙasar nan suka fita filin zaɓe domin su zaɓi wanda zai mulke su tsawon shekara huɗu. Mutum huɗu ne suka fi samun tagomashi. Na ɗaya, ɗan takarar jam'iyyar APC wadda ke kan mulki, Jagaban Borgu, Bola Ahmed Tinubu. Na biyu Wazirin Adamawa Atiku Abubakar na PDP, na uku Peter Obi, na LP, sai na hudu Injiniya Rabiu Kwankwaso na NNPP. Hukumar zaɓe ta ƙasa ta bai wa mutane miliyan 93 katin zaɓe. Amma da aka zo hakikanin zaven, kashi 27 ne suka fito. Da quri'ar Tinubu da Atiku da…
Read More
Kotu ta tsige ɗan Majalisar Wakilai daga Adamawa

Kotu ta tsige ɗan Majalisar Wakilai daga Adamawa

Kotun Ɗaukaka Ƙara mai zamanta a Abuja ta tsige ɗan Majalisar Wakilai daga Jihar Adamawa, wato Hon. Jingi Rufai, na jam'iyyar PDP. Kafin wannan lokaci, Jingi Rufai shi ne mai wakiltar Mubi ta Arewa, Mubi ta Kadu da Maiha a Majalisar Wakilai ta Ƙasa. Kotun ta yanke hukuncin haka ne a zaman da ta yi a ranar Talata, inda ta bayyana ɗan takarar jam'iyyar APC, Hon. Jaafar Magaji, a matsayin wanda ya lashe zaɓe. Kotun ta kuma bai wa hukumar zaɓe IMEC umarni a kan ta miƙa wa Magaji shahadar lashe zaɓen ba tare da wani jinkiri ba. Wannan na…
Read More
Dalilin Sanata Ndume na ficewa daga zauren Majalisa a fusace

Dalilin Sanata Ndume na ficewa daga zauren Majalisa a fusace

Da alama dai abubuwa ba su tafiya yadda ya kamata wa Majalisar Dattawan Nijeriya musamman ganin yadda shugabanin majalisar suka shiga ganawar sirri mintoci ƙalilan da fara zaman majalisar a ranar Talata. Yayin zaman Majalisar a ranar Talata an ga Mai Tsawatarwa na Majalisar, Sanata Ali Ndume (APC Borno ta Kudu), ya yi ƙoƙarin nusar da Majalisar dangane da kurakuran da ake zargi Shugaban Majalisar, Godswill Akpabio ya tafka ba tare da an yi gyara ba. Kuskuren da Ndume ke nufi shi ne kan batun ƙudirin da Sanata Summaila Kawu (NNPP Kano ta Kudu) ya gabatar a majalisa kan buƙatar…
Read More
‘Yan Majalisar Wakilai sun mayar da martani kan ƙorafe-ƙorafen da ake yi game da batun saya musu motocin alfarma

‘Yan Majalisar Wakilai sun mayar da martani kan ƙorafe-ƙorafen da ake yi game da batun saya musu motocin alfarma

Majalisar Wakilai ta ƙasa ta mayar da martani a kan ce-ce-ku-cen da 'yan ƙasa ke yi game da batun saya wa mambobinta su 360 sabbin motocin alfarma. A cewar Majalisar, za a sayi motocin ne don aikin ofis, kuma kuɗin da ake cewa za a sayo motocin bai kai yadda ake zuzutawa ba. A hirarsu da BBC, Honorabul Kabiru Alasan Rurum mai wakiltar ƙananan hukumomin Rano da Bunkure da Kibiya daga jihar Kano a Majalisar, ya ce: "Tun da mu ne karkatacciyar bishiya mai daɗin hawa kusan duk abubuwan a kanmu yake, ya kamata idan za a yi abu a…
Read More
Kotu ta tsige sanatan Adamawa daga kujerarsa

Kotu ta tsige sanatan Adamawa daga kujerarsa

Kotun Ɗaukaka Ƙara mai zamanta a Abuja, ta tsige Sanata Ishaku Abbo mai wakiltar Adamawa ta Arewa daga kujerarsa. Kotu ta yanke hukunci kan shari'ar ne a ranar Litinin inda ta karɓe kujerar Sanatan Adamawa ta Arewa daga hannu Abbo tare da bayyana ɗan takarar jam'iyyar PDP, Amos Yohanna a matsayin wanda ya lashe zaɓen. Da yake ysokaci jim kaɗan bayan hukuncin da kotun ta yanke, Abbo ya yi alƙawarin zai yi sanarwa a shafinsa na facebook. Daga nan ya ui kira ga jama'ar mazaɓarsa kan cewa kowa ya kwantar da hankalinsa.
Read More
Tinubu ya nemi Kotun Koli ta watsar da ƙarar Atiku bisa rashin bin ƙa’ida

Tinubu ya nemi Kotun Koli ta watsar da ƙarar Atiku bisa rashin bin ƙa’ida

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya buƙaci Kotun Kolin Nijeriya da ta yi watsi da ƙarar da ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar ya shigar, na ƙalubalantar sakamakon zaɓen shugaban ƙasa da aka gudanar a ranar 25 ga watan Fabrairu. Lauyoyin Tinubu ƙarƙashin jagorancin Wole Olanipekun (SAN) ne suka bayyana hakan, wanda a martanin da Atiku ya ɗaukaka, ya buƙaci Kotun Kolin ta yi watsi da ɗaukaka ƙarar da ya shigar na cin zarafi. A cikin ƙarar da Atiku ya shigar, ya buƙaci Kotun Kolin ta soke hukuncin da kotun sauraren ƙararrakin zaɓen shugaban…
Read More