Da Ɗumi-Ɗumi: Gwamnatin Kano ta sake sassauta dokar hana fita daga 6 zuwa 6

Spread the love

Daga RABI’U SANUSI

Gwamnatin Jihar Kano ta ƙara sassauta dokar hana zirga-zirga daga ƙarfe shidda na safiya zuwa shidda na Yamma.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ne na Jihar Kano ya bayyana haka a taron majalisar zartawa dake gudana yanzu a fadar gwamnatin Kano.

Gwamna Abba Kabir ya ce wannan ya biyo bayan taron majalisar tsaro da ya gudana yau ɗin nan kafin fara taron majalisar ta zartarwa da yake gudanar.

By ukarofi