
Daga BELLO A. BABAJI a Abuja
Tawagar ‘yan ƙwallon ƙasar Senegal ta lashe kofin gasar ƙasashen Nahiyar Afirka (AFCON) na 2025.
Hakan ya biyo bayan doke Moroko da ce 1 da nema a zangon ƙarin lokaci bayan shafe mintina 90 da ɗoriya ba tare da ɗayansu ya zura ƙwallo a raga ba.
Ɗan wasa Pape Gueye ne ya zura wata ƙayatacciyar ƙwallo a ragar Moroko, wanda hakan ya ƙayatar da masu kallo.
Wannan shi ne karo na biyu da Senegal ta lashe gasar a tarihinta tun bayan samun na farko a 2021.
