*Yadda gwamnonin wasu jihohi ma ke fuskantar makomarsu
Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja
A safiyar Juma’a, 12 ga Janairu, 2024, Kotun Kolin Tarayyar Nijeriya ta yanke hukunci mafi sarkakiya, tsumayi da zulumi a babban zaben kasar na 2023, wato shari’ar zaben Gwamnan Jihar Kano da ke arewacin kasar. Bugu da kari, a Juma’ar ce kuma Kotun Kolin ta yanke hukunci kan zaben kujerun gwamnan jihohin da suka hada da Legas, Zamfara, Filato, Ebonyi, Bauchi da Kuros Ribas, kamar yadda alkalan kotun suka sanar.
A karshen watan Disamba ne dai Kotun Kolin ta jingine hukunci akan karar da Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya daukaka yana mai kalubalantar hukuncin Kotun Daukaka Kara da Kotun Kararrakin Zabe na jihar, wadanda ta suka tuve shi daga mukaminsa.
Kotun Kolin mai alkalai biyar na Kotun Daukaka Kara a karkashin jagorancin Mai Shari’a John Okoro ya jinkirta hukuncin ne bayan da bangarori biyun suka gabatar da takaitaccen ba’asinsu.
A watan Satumba, Kotun Zabe ta soke nasarar Yusuf, dan takarar jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP) a zaben gwamnan da aka yi ranar 18 ga Maris, 2023. Kotun ta kuma tabbatar da Nasiru Gawuna na Jam’iyyar All Progressive Congress (APC) a matsayin zababben gwamnan Kano.
A ranar 13 ga Nuwamba, Kotun Daukaka Kara ta amince da hukuncin da kotun ta yanke. A hukuncinta ta kuma ce karar da Abba Yusuf ya shigar ya saba wa dokar zabe, saboda bai cancanta ya tsaya takara ba, amma gwamnan ya garzaya zuwa Kotun Koli, domin neman a wargaza hukuncin.
Hukuncin da Kotun Kolin ta yanke shine ya kawo karshen takaddamar, domin babu sauran daukaka kara.
Siyasar Kano:
Tun bayan da kotun farko ta soke zaben dan takarar jam’iyyar ta NNPP, Abba Kabir Yusuf, ne siyasar Jihar Kano ta hautsine, saboda yadda ake ganin NNPP a karkashin tafiyar siyasar Kwankwasiyya, wacce tsohon Gwamnan Jihar Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya ke jagoranta ta taka muhimmiyar rawa wajen kwace mulki daga hannun gwamnatin APC mai mulkin jihar a lokacin kuma mai mulkin Gwamnatin Tarayya a lokacin zaben da kuma yanzu. Mafi yawan masu nazari na kallon lamarin a matsayin wata gagarumar rawar siyasa.
To, amma jim kadan bayan rantsar da gwamnatin, sai ta hau yin rusau, inda ta rushe wasu gine-gine na ’yan kasuwa ba tare da bin ka’ida ba; lamarin da ake kallo a matsayin huce haushi kan gwamnatin da ta gabata a karkashin tsohon Gwamnan Jihar, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, wanda kuma a yanzu shine Shugaban APC na Kasa. Tuni dai kotu ta yanke hukuncin biyan wadanda aka yi wa rusau din diyya na Naira Biliyan 30.
Wannan rusau ya jefa fargaba a zukatan wasu ’yan kasuwa. To, kasancewar Kano jiha ce ta kasuwanci, wacce har ake yi wa lakabi da Cibiyar Kasuwanci a Nijeriya, babu shakka rusa dukiyar ’yan kasuwa zai iya shafar kima da mutuncin kowacce gwamnati. Don haka ba abin mamaki ba ne, idan aka ga ’yan kasuwa su na murna, idan Kotun Koli ta kori gwamnatin NNPP a Kano.
Idan kuwa Kotun Koli ta tabbatar da jam’iyyar, to hakan na nufin jam’iyyar ta NNPP mai tasowa za ta iya yin karfin da ba a yi tsammani ba a siyasar yankin Arewa maso Yamma ko ma Arewan bakidaya, saboda yadda Kano ke da tasiri a Nijeriya ta kowacce fuska, har ma a na yi ma ta kirari da Jalla Babbar Hausa ko Ta Dabi Cigari Ko Da Me Ka Zo An Fi Ka ko kuma Tumbin Giwa. Hakika wannan wata dama ce babba ga Kwankwasiyya ta yi sheka da kwai ta kyankyashe a siyasar Nijeriya.
Bugu da kari, faduwar APC da dan takararta, Nasiru Yusuf Gawuna, babban nakasu ne ga siyasar Gandujiyya; a lokaci guda kuma nasarar APC a kotun, babban kwarjini ne ga siyasar Gandujiyyar.
Tsaro:
Idan aka yi la’akari da irin kalaman da wasu mabiya siyasar Kwankwasiyya suka furta, za a iya cewa, a shirye suke da su yi duk abinda suka ga dama matukar Kotun Koli ba ta ba su nasara a hukucin ba. Tsohon mai taimaka wa Gwamna Abba da tsohon kwamishinansa sun yi ikirarin kashe alkalai matukar ba a su abinda suke so ba. Ita ma wata yarinyar mabiyar Kwankwasiyya daga Jihar Kano ta yi ikirarin dauka bom ta yi kunar bakin wake matukar ba a bai wa Abba nasara ba. Shi kansa daya daga cikin alkalan Kotun Zaben Kano a yayin da yake yanke hukunci ya suffanta ’yan Kwankwasiyya da ’yan bindigar daji ko masu garkuwa da mutane da ake fama da su a arewacin Nijeriya, saboda yadda ya ce, sun yi musu barazana kuma sun kore su daga Kano.
Wadannan misalai ne da ke nuni da irin hatsarin matsalar tsaron da watakila ’yan Kwankwasiyya za su iya haifarwa a jihar, idan Abba da NNPP suka fadi a kotun. Kada a manta, Kwankwasiyya siyasa ce, ba jam’iyya ba. Ma’ana; ta na kama da akida kenan. Don haka akwai jan aiki a gaban jami’an tsaro kenan.
A jiya Alhamis, Kwamishinan ’Yan Sanda na Jihar Kano, Muhammad Usaini Gumel, ya yi taron manema labarai, inda ya bayyana cewa, rundunarsa ta shirya tsaf, don maganin duk wani wanda ya tayar da tarzoma bayan yanke hukuncin, inda aka baja jami’an tsaro a dukkan fadin jihar.
Kotun Koli:
Tabbas Kotun Kolin Nijeriya ta shiga tsaka-mai-wuya a wannan shari’ar, domin duk irin hukuncin da ta yanke sai an zarge ta da aikata rashin adalci.
Idan alkalan kotun suka ce NNPP ce ta yi nasara, to za a ce barazabar tsaro da mabiya Kwankwasiyya suka yi musu ce ta yi tasiri. Idan kuma kotun ta bai wa APC nasara, to za a ce ta hada baki da Shugaban Kasa da mataimakinsa Kashim Shettima, wanda ake zargi da kokarin bayan siyasar Kwankwaso da kuma shugaban APC na Kasa, Ganduje, wajen yin rashin adalci.
Bari mu duba gwagwarmayar sauran jihohin da ake yanke hukunci a yau kamar haka:
Mutfwang da Goshwe:
A ranar 9 ga Janairu, 2024, Kotun Koli ta tanadi hukunci a cikin karar da Gwamnan Jihar Filato, Caleb Mutfwang ya shigar, na neman soke hukuncin da Kotun Daukaka Kara ta yanke wanda ya soke zabensa. Wani kwamitin alkalai biyar karkashin jagorancin mai shari’a John Okoro ya jngine hukuncin bayan sauraron hujjojin da jam’iyyu suka yi akan karar da aka shigar. Gwamnan ta bakin lauyansa, Kanu Agabi, ya roki kotun da ta tabbatar da hukuncin da kotun daukaka kara ta yanke, sannan ta yi watsi da hukuncin kotun daukaka kara saboda wadanda ake kara ba su da hurumin tambayar yadda jam’iyya ke zaben shugabanninta na jihohi.
Ya ce wadanda ake kara (Nentawe Goshwe da jam’iyyar All Progressives Congress) ba za su iya cewa gwamnan bai ci adadin kuri’un halal da aka ba shi ba a daidai lokacin da suka ce zaben bai inganta ba. A watan Nuwamba ne kotun daukaka kara da ke Abuja ta kori Mutfwang tare da umurci hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa ta ba da takardar shaidar cin zabe ga Goshwe amma gwamnan ya garzaya kotun koli domin neman hakkinsa.
Lawal da Matawalle
A watan Nuwamban da ya gabata ne kotun daukaka qara ta soke zaben gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal. An ayyana Lawal na babbar jam’iyyar adawa ta PDP a matsayin wanda ya lashe zaben gwamna da aka gudanar a ranar 18 ga watan Maris. A wani gagarumin nasara da ya kawar da Bello Matawalle na Jam’iyyar APC a lokacin, ya samu kuri’u 377,726. Matawalle ya samu kuri’u 311,976. Dan takarar na PDP, wanda a yanzu yake rike da mukamin karamin ministan tsaro, ya zargi INEC da murguda nasarar da ya samu a zaben, ta hanyar kin sanya sakamakon wasu unguwanni.
A wani hukunci da ta yanke a baya a ranar 18 ga watan Satumba, kotun sauraron kararrakin zabe ta jihar Zamfara ta ce karar ba ta da wani cancanta. Yayin da take tabbatar da nasarar Lawal, kotun ta bayar da tarar N500,000 ga wadanda suka shigar da kara. Wani Matawalle da bai gamsu ba, kamar yadda masu lura da al’amura ke zato, ya kai karar kotun daukaka kara da ke Abuja, domin qalubalantar hukuncin da qaramar kotun ta yanke. Mai shari’a Sybil Nwaka ya umurci INEC da ta gudanar da sabon zabe a kananan hukumomi uku na jihar, inda a baya ba a gudanar da zabukan ba, ko kuma ba a kidaya sakamakon zabe daga rumfunan zabe daban-daban. Amma gwamnan ya garzaya kotun koli domin neman hakkinsa.
Muhammad Abubakar da Bala
Haka kuma a watan Nuwamba, Kotun Daukaka Kara ta tabbatar da nasarar Gwamna Bala Mohammed na jihar Bauchi a zaben gwamnan da aka yi a ranar 18 ga watan Maris. Dan takarar gwamna na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ne, Sadique Abubakar, ya shigar da karar ne biyo bayan hukuncin kotun da ta tabbatar da nasarar Mohammed. Alkalan kotun guda uku sun hadu baki daya, inda suka bayar da kyautar ba tare da bata lokaci ba, domin kotun ta ce kowane mai shari’a ya biya kudinsa. Alkalin kotun, Mai shari’a Chidi Nwaoma Uwa, ya karanta hukuncin ne bisa umarnin wanda ya shigar da kara a gaban kotun daukaka kara.
A kara ta daya, wanda ya shigar da kara ya roki a soke zaben saboda ba a cike fom da takardun da aka yi amfani da su a zaben yadda ya kamata ba. Kotun ta yanke hukuncin cewa wanda ya shigar da kara ya kasa tabbatar da wannan zargi tare da hujjojin da ake bukata.
Sanwo-Olu da GRV, Jandor
Kotun Daukaka Kara da ke Legas a watan Nuwamba ta tabbatar da hukuncin da kotun ta yanke, inda ta tabbatar da dawowar Babajide Sanwo-Olu da Obafemi Hamzat a matsayin Gwamna da Mataimakin Gwamnan Jihar Legas. Alkalan kotun daukaka kara a cikin hukuncin da ya yanke sun yi watsi da karar da jam’iyyar PDP da na Labour (LP) suka shigar saboda rashin cancanta. A watan Maris ne INEC ta ayyana Sanwo-Olu a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan Legas. Sanwo-Olu ya samu kuri’u 762,134 inda ya doke abokin hamayyarsa na LP Gbadebo Rhodes-Vivour wanda aka fi sani da GRV wanda ya samu kuri’u 312,329. Dan takarar Jam’iyyar PDP Abdulazeez Adediran wanda Jandor ya zo na uku da kuri’u 62,449.
Ba su gamsu da sakamakon zaven ba, ’yan takarar LP da PDP sun tuntubi kotun sauraren kararrakin zabe ta Jihar Legas don soke nasarar Sanwo-Olu. A hukuncin da ta yanke a ranar 25 ga Satumba, kotun ta yi watsi da karar Adediran da Rhodes-Vivour na neman soke nasarar Sanwo-Olu a zaben. Ba su ji dadin hukuncin ba, su biyun sun tunkari kotun daukaka kara amma babbar kotun ta yi watsi da karar nasu. Daga bisani dukkan mutanen biyu sun garzaya kotun kolin da ake sa ran za ta yanke hukunci a ranar Juma’a.
Nwifuru da Odii
A ranar Talata ne Kotun Koli ta jingine hukunci a karar zaben Gwamnan Jihar Ebonyi. A watan Nuwambar da ya gabata ne Kotun Daukaka Kara da ke zamanata a Legas ta tabbatar da zaben Francis Nwifuru na jam’iyyar APC a matsayin zababben Gwamnan Ebonyi a zaben gwamnan da aka yi ranar 18 ga watan Maris. Kwamitin mutum uku karkashin jagorancin mai shari’a Jummai Sankey, a hukuncin da ta yanke, ya yi watsi da karar da Chukwuma Odii na jam’iyyar PDP ya shigar tare da tabbatar da hukuncin da kotun ta yanke a baya amma dan takarar na PDP ya garzaya kotun koli domin neman hakkinsa.
