Matatar Ɗangote ta fara tunanin fasa sayar da fetur a Nijeriya

Spread the love

Daga MAHDI M. MUHAMMAD

Matatar man Dangote za ta iya fitar da man fetur zuwa ƙasashen waje sakamakon ƙ

in amincewa da Kamfanin Man Fetur na Nijeriya, NNPCL, ya yi na zama babban mai sayen kayanta.

Kamfanin mai na NNPC, a wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Olufemi Soneye, ya fitar a ranar Asabar, ya ce ba za ta sayi man Dangote ba, sai dai idan ya yi arha fiye da na kasuwannin duniya.

Wannan ya saba ikirari da Shugaban Rukunin Dangote, Aliko Dangote ya yi na cewa matatar ta na jiran NNPC don fara fitar da kayanta.

A ranar Asabar ɗin da ta gabata ne kamfanin mai na kasa NNPC ya bayyana cewa, zai sayi mai daga matatar man ne kawai idan farashin kasuwar man ya zarce farashin da ake sayarwa a Nijeriya.

Kamfanin na NNPC ya kuma bayyana cewa Dangote da sauran matatun mai na cikin gida suna da ’yancin sayar da su kai tsaye ga kowane ɗan kasuwa a kan wanda ya ke son saye, inda ya ce ba shi da wani buri ko niyyar zama mai raba wa kowani mahalli a cikin yanayin kasuwa mai ’yanci.

Kamfanin dai na mayar da martani ne ga wata sanarwar manema labarai da ƙungiyar kare haƙƙiin Musulmi ta fitar, inda ta yi ikirarin cewa kamfanin na NNPC na lalata matatar man Dangote.

MURIC ta bayyana cewa, canje-canjen farashin man fetur da hukumar NNPC ta yi a baya-bayan nan, zai hana matatar farashin farashi mai sauki, kuma kamfanin ya zama tilo mai cin gashin kan dukkan kayayyakin da ake samu daga matatar.

Da yake mayar da martani, NNPC ya ce, “Rundunar kasuwannin duniya ne ke ƙayyade farashin man fetur daga kowace matatar mai da ta haɗa da matatar Dangote.

By ukarofi