Daga MAHDI M. MUHAMMAD
Jam’iyyar PDP reshen jihar Zamfara na zargin Gwamna Bello Matawalle na shirin yin maguɗin zaɓe na sahihancin sakamakon zaɓen mahaifarsa Ƙaramar Hukumar Maradun.
Jam’iyyar PDP a wata sanarwa da ofishin yaɗa labarai na Dauda Lawal ta fitar, ta ce, gwamnan ya tuntuɓi manyan jami’an INEC a ƙoƙarinsa na ganin an bayyana sakamakon zaɓen.
Ta kuma yi zargin cewa gwamnan, ɗan jam’iyyar APC, ba ya son amincewa da shan kaye cikin kwanciyar hankali.