Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja
Gwamnan jihar Bauchi, Bala Mohammed, ya ce shawarar jam’iyyar PDP ta bai wa kudu damar tsayar da dan takarar shugaban ƙasa a 2027 sadaukarwa ce da aka yi domin haɗin kai.
A ranar Litinin, kwamitin ƙoli na PDP, wato National Eɗecutive Committee (NEC), wanda shi ne mafi girman matakin yanke hukunci a jam’iyyar, ya amince da mika tikitin shugaban ƙasa ga yankin Kudu, tare da barin kujerar shugabancin jam’iyyar a arewa.
Wannan tsarin ya cire Bala Mohammed da sauran manyan ‘yan PDP na arewa da ake cewa suna da sha’awar kujerar shugaban ƙasa.
Da yake zantawa da manema labarai a Bauchi ranar Talata, Mohammed ya ce siyasa ya kamata ta kasance kan ginshiƙin haɗin kai, ba kan son zuciya ba.
Ya ce: “Na gamsu ƙwarai da wannan ƙudiri, saboda ni ma ina cikin tsarin, dabarun, da kuma yadda aka aiwatar da shi. Mun yanke shawarar gudanar da babban taron jam’iyya a Ibadan, jihar Oyo, ranar 15 ga Nuwamba, tare da wani taron NEC a ranar 15 ga Oktoba.”
Ya ƙara da cewa: “Mun kuma yarda da ci gaba da tsarin rabon mukaman jam’iyya da ake amfani da shi, tare da mika tikitin shugaban ƙasa ga kudu domin tabbatar da zaman lafiya, fahimtar juna, da kuma haɗin kai.”
Ya ce: “Siyasa ba wai game da son zuciya ba ne. Siyasa tana da alaƙa da cika manufofi bisa tsarin jam’iyya, kundinta da kuma ci gaban kasa.”
