Yawan Falasɗinawan da aka kashe a Gaza ya haura 73,000

Spread the love

Adadin Falasɗinawan da suka rasa rayukansu sakamakon hare-haren sojin Isra’ila a Zirin Gaza ya kai mutane 73,032, yayin da waɗanda suka jikkata suka kai 173,357, tun bayan fara yaƙin a ranar 7 ga Oktoban shekarar 2023, kamar yadda majiyoyin kiwon lafiya a yankin suka bayyana.

Bayanan da hukumomin lafiya suka fitar sun nuna cewa asibitocin Gaza sun karɓi gawawwaki tara da kuma mutane 41 da suka samu raunuka a cikin sa’o’i 24 kacal da suka gabata, abin da ke nuna cewa har yanzu rikicin na ci gaba da jawo asarar rayuka da raunata dubban mutane.

Majiyoyin sun ƙara da cewa tun bayan fara tsagaita wuta a ranar 11 ga Oktoban bara, adadin Falasɗinawan da aka kashe ya kai 1,021, yayin da yawan waɗanda suka samu raunuka ya kai 3,249. Haka kuma, an samu nasarar ciro gawarwaki 784 daga ƙarƙashin baraguzan gine-gine da wuraren da aka lalata a wannan lokaci.

Rahoton ya bayyana cewa har yanzu akwai mutane da dama da ake kyautata zaton sun mutu ko kuma suka jikkata amma suke maƙale a ƙarƙashin baraguzan gine-ginen da hare-haren suka rushe, ko kuma a kan tituna da wuraren da ba a iya isa gare su.

A cewar jami’an lafiya, motocin ɗaukar marasa lafiya da ƙungiyoyin agaji na ceto na fuskantar matsaloli wajen isa wasu yankuna saboda tsananin lalacewar ababen more rayuwa da kuma matsalolin tsaro, lamarin da ke jinkirta kai dauki ga waɗanda suka tsira da rayukansu.

Fiye da shekara biyu da rabi kenan da fara wannan rikici, inda hare-hare masu tsanani suka yi sanadiyyar lalata gidaje, makarantu, asibitoci da sauran muhimman kayayyakin more rayuwa a faɗin Zirin Gaza.

Yayin da ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan adam da na jin ƙai ke ci gaba da kira ga duniya da ta ƙara matsin lamba domin kawo ƙarshen tashin hankalin, al’ummar Gaza na ci gaba da rayuwa cikin mawuyacin hali na rashin matsuguni, ƙarancin abinci, magunguna da sauran muhimman abubuwan rayuwa.

Sabbin alkaluman da aka fitar sun sake nuna girman asarar da rikicin ya haifar ga fararen hula, musamman yara da mata, waɗanda suka kasance cikin waɗanda suka fi shan wahala tun bayan barkewar yaƙin a ƙarshen shekarar 2023.

By ukarofi