Ɗalibi Aminu zai gana da Buhari bayan sako shi daga kurkuku

Daga BASHIR ISAH

An sako ɗalibin nan, Aminu Mohammed Adamu, wanda aka tsare tare da maka shi a kotu don ya soki matar Shugaban Ƙasa, Aisha Buhari.

Rahotannin da Manhaja ta samu sun nuna, Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari zai gana da Aminu kafin daga bisani a miƙa shi ga ‘yan uwansa.

Idan dai ba a manta ba, kimanin makonni biyu da suka gabata jami’an tsaro suka damƙe ɗalibin inda suka ɗauke shi zuwa Abuja sakamakon sukar da ya yi wa Aisha Buhari a shafinsa na Tiwita, inda ya ce Aisha ta ci kuɗin talakawa ta yi ɓul-ɓul.

A ranar Talatar da ta gabata aka gurfanar da Aminu a wata Babbar Kotun Abuja don ya fuskanci shari’ar zargin da ya aikata.

Lamarin da ya haifar da ce-ce-ku-ce a tsakanin jama’a a ciki da wajen ƙasa.

Daga bisani, Aisha ta janye ƙarar da ta shigar kan Aminu bayan da wasu manyan ƙasa suka sanya baki ciki batun, kamar yadd lauyanta ya bayyana.