INEC za ta fara raba Katin Zaɓe 12 ga Disamba

Daga BASHIR ISAH

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC), ta ce, ta rarrabe tsarin karɓar Katin Zaɓe (PVC) zuwa matakin gundumomi daga ranar 6 ga Janairun 2023.

Kazalika, hukumar ta ce daga ranar 12 ga Disamba, 2022 za ta soma raba wa waɗanda suka yi rajista Katin Zaɓe a dukkan ƙananan hukomimi 774 da ake da su a faɗin ƙasa.

INEC ta bayyana hakan ne cikin sanarwar da ta fitar Juma’ar da ta gabata, inda ta ce an cimma matsayar haka ne a wajen taron da ta gudanar kwanan nan a Legas.

Sanarwar wadda ta sami sa hannun Kwamishinan hukumar, Festus Okoye, ta nuna za a gudanar da shirin karɓar katin zaben ne a cibiyoyin rajista/gundumomi 8,809 da ake da su a faɗin ƙasar ya zuwa watan Janairu mai zuwa.

“Hukumar ta tsayar da ranar Litinin, 12 ga Disamban 2022 zuwa Lahadi, 22 ga Janairun 2023 a matsayin wa’adin da za a karɓi Katin Zaɓe a ofisoshin INEC da ake da su a ɗaukacin lananan hukumomi 774 da ke faɗin ƙasa,” inji sanarwar.