ASUU ta janye yajin aiki

Spread the love

Daga BASHIR ISAH

Ƙungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU) ta janye yajin aikinta don bai wa mambobinta damar komawa bakin aiki.

Duk da dai kungiyar ba ta ba da sanarwar hakan a hukumance ba, amma jaridar Punch ta tattaro cewar an cimma matsayar janye yajin aikin ne bayan tattaunawar da shugabannin ƙungiyar na ƙasa suka yi a Abuja.

Majiyar Punch ta tabbatar cewa, ‘Lallai an janye yakin aikin.”

Sai dai majiyar ta ce a saurari shigaban ASUU na ƙasa domin ƙarin bayani da safiyar Juma’a.

Da alama dai ƙungiyar ta janye yajin aikin ne domin biyayya ga umarnin Kotun Ɗaukaka Ƙara inda ta buƙa i malamai su koma baki aiki.

Idan dai ba a manta ba, Manhaja ta rawaito ASUU ta soma yajin aikin nata ne ran 14 ga Fabrairun 2022, wato kimanin watanni takwas da suka gabata da zummar neman haƙƙoƙinta a wajen gwamnati.

By Editor