Ba ƙaramar kasada Tinubu ya yi ba wajen naɗa ni minista – Wike

Spread the love

Daga MAHDI M. MUHAMMAD

Ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya bayyana irin salon siyasa da kalubalen da ya fuskanta a nadin da shugaba Bola Tinubu ya yi masa. Wike ya yarda cewa Tinubu ya yi kasada sosai wajen nada shi ministan Abuja, inda ya nuna cewa akwai adawa sosai a matakin.

Wike ya jaddada muhimmancin ajiye adawa a gefe don cigaban kasa. Ya kuma bukaci jama’a da su amince da matakin da shugaba Buhari ya dauka, yana mai cewa duk da cewa ba shi ne zabi mafi kyau ba, amma babu wani zabi.

Wike ya kuma nuna godiya ga shugaban majalisar da sauran membobin da suka mutunta shawarar shugaban ba tare da sanya wasu sharudda ba.

Da yake magana akan zargin cin amana da wasu bangarori ke yi, Wike ya bayyana cewa bai ci amanar jam’iyyar PDP ba. Maimakon haka, ya yi ikirarin cewa shi da wasu sun tsaya tsayin daka kan shawararsu, suna tabbatar da cewa an cika wasu sharudda kafin su dauki wasu matakai.

Wike ya yi kira da a hada kai da goyon bayan shugaban kasa, yana mai jaddada bukatar yin aiki tare ba tare da la’akari da bangaren siyasa ba wajen cigaban Nijeriya.

By Editor