Gwamnatin Tarayya na shirin buɗe cibiyoyin mata a jihohin ƙasar

Spread the love

Darakta Janar ta cibiyar cigaban mata ta Maryam Babangida ta sanar da shirin cibiyar na samun haɗin kai da Majalisar Ɗinkin Duniya da Ofishin Jakadancin Kanada domin buɗe wasu cibiyoyin a faɗin ƙasar.

Ta yi wannan jawabin a wani taron ƙarawa juna sani na kwana biyu da a ka shirya ga Kwamishinonin mata na faɗin jihohin Nijeriya 36.

Dakta Asabe Bashir wadda itace Darakta Janar, ta bayyana cewa yin haka zai ƙara wa mata ƙwarin gwiwa domin shiga harkoki a dama da su.

Wakiliyar shugabar mata na Majalisar Ɗinkin Duniya, Zephaniah Aura ta jaddada yadda majalisar ta dage wajen ganin mata sun samu cigaba musamman a Nijeriya.

Ta ƙara da cewa, cibiyoyin nan da za a buɗe, za su zama wuri ne da mata za su haɗu su rinƙa tattaunawa a kan al’amuran da ya shafe su ta ɓangarori da dama misali, shugabanci, sana’a da sauran su. Ta bayyana za a fara buɗe waɗannan cibiyoyin a garin Ekiti, Kwara, Ebonyi da Kaduna.

Jakadan ƙasar Kanada a Nijeriya ya bayyana cewa waɗannan cibiyoyin za su taimaka ƙwarai ganin mata sun samu damammaki musamman a lamuran shugabanci.

A ƙarshe ya bayyana cewa su yi amfani da wannan taron ƙara wa juna sanin domin koyon sabbin abubuwan da za a koyar.

By ukarofi