Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja
Majalisar dattijan Nijeriya ta buƙaci Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, da ya dakatar da rushe gidaje a Abuja har sai an kammala binciken da kwamitin riƙon ƙwarya na majalisar zai gudanar.
An cimma wannan matsaya ne a ranar Alhamis bayan wani ƙudiri da Sanata Ireti Kingibe ta gabatar, inda ta nuna damuwa cewa rusau a FCT sun ɗauki wani mummunan yanayi.
Kingibe ta dage cewa akwai buƙatar Majalisar Dattijai ta sa baki.
“Har ila yau, akwai damuwa na cewa ana rusau a Abuja ba bisa ƙa’ida ba, kuma wasu mutane da dama sun gamu da matsananciyar wahala sakamakon rushe gidaje da ya jawo asarar kadarori da suka kai daruruwan biliyoyin Naira.
“Mahukuntan FCT, sun ce rushe-rushen ya samo asali ne saboda gine-ginen da aka yi babu izini da kuma rashin ci gaba da gine-gine a filayen da aka raba wa mutane daga mahukuntan FCT.
Sanata Kingibe ta ce amma an shiga damuwa kan zargin yanzu ana rushe-rushe ƙara zube ba bisa ƙa’ida ba.
“Haka kuma ana damuwa da cewa, a halin yanzu, za a rushe wani gini mai suna Merss Paulosa, wanda Marigayi Kanal Paul Osang Kwanwa na Bebo. Kuma daga bayanan da aka samu, filin da ake magana akai an ba shi tun shekarar 1984 tare da dukkan takardun da su ka dace.”
“Mai wannan gini ya kasance ɗan Nijeriya mai kishin ƙasa wanda ya yi wa kasa hidima, kuma yana daga cikin zaɓaɓɓun farko na Kwalejin Tsaro ta Nijeriya da ke Kaduna, mai lamba 001.”
Bayan gabatarwar Kingibe, sanatan da ke wakiltar Kogi ta Yamma, Sunday Karimi, ya yi watsi da ƙudirin, inda ya buƙaci abokan aikinsa kada su hana minista aiwatar da ayyukansa.
Ya ba da shawarar a gudanar da bincike kan rusau da aka yi a baya zuwa yanzu.
A jawabinsa, Shugaban Majalisar Dattijai, Godswill Akpabio, ya ce wa sanatan da ta cire son zuciya, ya zama mai kishin ƙasa, yana mai cewa ba za a fara yi wa mutane ɓarna ba, sannan a gudanar da bincike daga baya.
Akpabio ya nuna damuwa cewa gwamnati na iya fuskantar shari’a daga waɗanda abin ya shafa.
Bayan haka, ya bayar da umarnin cewa a dakatar da rushe-rushen da ake yi a yanzu.
An kafa wani kwamitin riƙon ƙwarya ƙarƙashin jagorancin Sanata Barau Jibrin don binciken batun na rusau.
