Mambobin ADC sun shigar da ƙarar ƙalubalantar halascin jagorancin riƙo a jam’iyyar

Spread the love

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja

Wasu manyan mambobin jam’iyyar ADC guda uku sun shigar da ƙara a Babbar Kotun Tarayya dake Abuja inda suke ƙalubalantar jagorancin riƙon ƙwarya a ƙarƙashin tsohon shugaban Majalisar Dattawa, David Mark da aka kafa a jam’iyyar.

A takardar ƙarar, wadda aka rubuta a ranar 4 ga Yuli an ga yadda masu ƙarar, wato Adeyemi Emmanuel, Ayodeji Tolu da Haruna Isma’il suka nemi kotun da ta bayyana sahihanci ko rashin haka na jagorancin riƙon ƙwaryar.

Sun ce, Nwosu, wanda shi ne tsohon shugaban jam’iyyar, ba shi da damar kiran taron kwamitin ayyuka (NWC) ko na kwamitin majalisar zartarwar jam’iyyar (NEC) duba da cewa wa’adinsa a matsayin shugaba ya ƙare.

Haka kuma sun ce, jagororin riƙo ba su da damar yin aiki a matsayin halastattun shugabannin jam’iyya da aka amince da su, suna cewa an naɗa su ne a haramtaccen zama da tsohon shugaban ya jagoranta.

Akan haka ne suka buƙaci kotun da ta soke naɗin David Mark, Aregbesola da Abdullahi, saboda abu ne da aka yi ba bisa doka ba.

Sannan, sun nemi kotun ta haramta wa Hukumar Zaɓe (INEC) tabbatar da mutane ukun a matsayin jagororin riƙo a jam’iyyar.

By Babaji