Akwai matsala a tsaron bayan Liverpool – Klopp

Spread the love

Daga MAHDI M. MUHAMMAD

Mai horar da ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Liverpool, Jurgen Klopp ya amsa cewa dole ne tawagarsa ta sake lale, tare da ƙara ƙaimi a kan yadda ta ke tsaron baya, dai dai lokacin da ƙungiyar wadda ta ƙarƙare a matsayin ta biyu a kakar da ta gabata, ga fama da rashin nasara a wannan kaka.

Liverpool wadda yanzu haka ke matsayin ta 9 a teburin gasar Firimiya, bayan nasara a wasanni 2 kacal daga cikin 7 da ta doka a wannan kaka.

Ƙungiyar dai na ci gaba da shan caccaka musamman daga magoya baya, ganin yadda ta yi sake har ƙwallaye 14 suka shiga ragarsu a wasanni 9 da suka buga a wannan kaka, wanda ke nuna cewa a wasanni biyu ne kawai suka iya hana ƙwallo taba zarensu ba.

Ko a wasansu na ƙarshen mako, Liverpool ta bari ƙwallaye har 3 sun shiga ragarsu inda suka tashi ƙwallaye 3 da 3 a karawarsu da Brighton ranar Asabar, lamarin da ya sa yanzu Arsenal da ke a matsayi na 1 ta ba su ratar maki 11, Manchester City da ke matsayin ta 2 kuma ta ba su ratar 10.

A cewar Jurgen Klopp wajibi ne su zage damtse don fita daga matsalar da suke fuskanta, wanda a cewar kocin na da nasaba da rashin tsaro a baya.

By Editor