An kama ɗan kasuwar Angola da hodar iblis a filin jirgin sama a Kano

Spread the love

Daga USMAN KAROFI

Hukumar yaƙi da sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta ƙasa (NDLEA) ta ce jami’anta sun kama wani ɗan kasuwa ɗan Angola mai suna Mbala Dajou Abuba, mai shekaru 42, a filin jirgin sama na Mallam Aminu Kano, yayin da yake ƙoƙarin safarar hodar iblis zuwa Turkiyya.

A cewar kakakin NDLEA, Femi Babafemi, wanda ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi, an kama Abuba ne a ranar Talata, 25 ga Fabrairu, 2025, yayin da yake ƙoƙarin shiga jirgin Egypt Air MS 880 zuwa Istanbul, Turkiyya, ta hanyar birnin Cairo.

Bayan an yi masa gwajin jiki, an gano cewa ya haɗiye hodar iblis. Daga nan ne aka sa ido a kansa har sai da ya fitar da kimanin kwanson hodar iblis guda 120, masu nauyin kilogiram 1.829.

Abuba ya bayyana cewa yana gudanar da kasuwancin kai kaya a cikin birane a Angola kafin ya tsunduma cikin harkar fataucin miyagun ƙwayoyi.

A wani samame makamancin haka, jami’an NDLEA sun kuma kama wani ɗan kasuwa mai sayar da kayan gyaran mota, Okeke Ebuka Igwe, yayin da yake ƙoƙarin aika hodar iblis mai nauyin kilogiram 1.10 zuwa Angola ta filin jirgin Murtala Muhammed da ke Legas.

Bugu da ƙari, wani mutum mai suna Ezechi Iyke Cyprian an kama shi yana ƙoƙarin jigilar hodar iblis mai nauyin kilogiram 5.40 a cikin motarsa kirar Toyota Sienna zuwa Owerri, jihar Imo.

A wani samame da aka yi a tashar jiragen ruwa ta Tincan da ke Legas, jami’an NDLEA sun gano kwalayen tabar wiwi nau’in Canadian Loud guda 128, waɗanda aka ɓoye a cikin katifu a wata mota ƙirar Toyota Venza da aka shigo da ita daga Canada.

NDLEA ta tabbatar da kama wanda ake zargi da mallakar wannan kayan, wani mutum mai shekaru 44 mai suna Bamidele Joseph, wanda yanzu haka yana hannun hukuma.

By ukarofi