An tsare likitan Nijeriya a Birtaniya bisa zargin ɗaukar bidiyon tsiraicin mata yayin tiyata

Spread the love

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD

Rundunar ’yan sandan Kent a Birtaniya ta kama kuma ta tsare tsohon daraktan Optimal Cancer Care Foundation na Legas, Dr. Olufemi Olaleye, bayan isa filin jirgin Gatwick daga Nijeriya a ranar Alhamis, 27 Nuwamba 2025.

Rahotanni sun tabbatar da cewa an cafke shi ne bisa zargin aikata laifukan fyaɗe ta hanyar ɗaukar bidiyon ayyukan sirri ba tare da izinin mata ba a lokacin da yake aiki a Ingila.

Hukumomin Kent Police sun tabbatar da kama likitan a ranar Talata, inda suka ce an yi masa tuhumar laifukan cin zarafi guda uku.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, Charles Harman, ya shaida wa Saturday PUNCH cewa an sanar da su dawowar wanda ake zargi daga Nijeriya, wanda ya sa suka je tashar jirgin suka kama shi nan take.

A cewar rundunar, wanda ake zargin — mai amfani da sunaye daban-daban irin su Frank, Femi da Francis — ya musanta laifukan a gaban kotun Medway Magistrates a ranar Asabar, 29 Nuwamba, kuma an umarci a tsare shi har zuwa zama na gaba a ranar 5 Disamba.

Tuhumar ya yi nuni cewa tsakanin Mayu 2004 da Yuli 2007, a Kent, wanda ake zargin ya ɗauki bidiyon mata yayin da suke yin ayyukan sirri da manufar samun fasiƙanci, duk da sanin cewa ba su amince a ɗaukar bidiyon su ba.

Binciken The PUNCH ya gano cewa yayin zaman Dr. Olaleye a Birtaniya, ya ɗauki bidiyon wasu mata a lokutan mu’amala, ciki har da wata matar aure da mijinta ya ci karo da hoton bidiyon da ya kai ga rugujewar aurensu. Ita ce ɗaya daga cikin shaidu uku da ‘yan sanda suka dogara da su.

Alƙalin kotu ya ce an tsare shi saboda yiwuwar gudu ko kuma sake aikata laifi, don haka za a sake duba umarnin tsarewa a ranar 2 Janairu 2026, kuma zaman shari’ar asali zai gudana a 21 Janairu 2026 a kotun Maidstone.

Kamen da aka yi wa Dr. Olaleye a Birtaniya ya biyo bayan doguwar taƙaddamar shari’a da ta wakana a Legas kan zargin laifukan fyaɗe. An gurfanar da shi a kotun laifukan jima’i da cin zarafi a 2022 kan zargin lalata ‘yar uwar matarsa, mai shekaru 15 zuwa 16 a lokacin.

Matarsa a lokacin, Aderemi Olaleye, ita ce shaida ta farko, inda ta bayyana cewa cin zarafin ya fara ne da koya wa yarinyar kallon hotunan batsa, daga bisani ya zarce zuwa taɓa ta ta hanyoyin da ba su dace ba, sannan kuma zuwa yi mata huɗuba ba tare da yardarta ba — galibi a wuraren da babu CCTɓ da tsakar dare.

Ta kuma yi zargin cewa wani lokaci yana bacci mata magunguna kamar Junior Aspirin da Phenergan domin ya sami damar aikata laifin. An kuma samu shaidar direban gida da ya ga yarinyar tana amai mai dauke da alamar maniyyi.

Cibiyar Mirabel ta tabbatar da samun raunuka da yankewar fata a gabanta.

A ranar 24 Oktoba 2023, Mai Shari’a Rahman Oshodi ya same shi da laifi, ya yanke masa hukuncin rayuwa a kurkuku, yana kiransa “maƙiyin al’umma” mai rashin nadama.

Sai dai a ranar 29 Nuwamba 2024, Kotun Daukaka Kara ta Legas ta rusa hukuncin, ta wanke shi, ta kuma soke dukkan tuhuma.

By ukarofi