02
Sep
Daga MAHDI M. MUHAMMAD Babbar Lauyar Gwamnatin Tarayyar Nijeriya, Beatrice Jeddy-Agba, ta bayyana cewa, Ma’aikatar Shari’ar ba ta samun wani kaso na kasafin kuɗi ba, don biyan basussukan shari’un da take gudanarwa ba. Jeddy-Agba, wacce kuma ita ce babbar sakatariya a ma’aikatar ta shari’ar ƙasar, ta bayyana hakan a Abuja, Babban Birnin Tarayya, a wani taron tattaunawa kan samun hanyoyin magance take haƙƙin bil’adama a Nijeriya. Taron mai taken ''Tattauna dabarun samun hanyoyin magance take haqqin bil'adama a Nijeriya" an shirya shi ne a bayan fagen taron ƙungiyar lauyoyin Nijeriya, NBA, da ke gudana a Abuja. Jeddy-Agba, wadda Enoch Simon,…
