01
Sep
Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau Jam’iyyar All Progressives Congress APC a Zamfara ta nesanta kanta daga zargin kitsa yunƙurin hamɓarar da Gwamna Dauda Lawal kamar yadda jam’iyyar PDP mai mulki a jihar ta yi zargi. Sakataren Yaɗa Labarai na Jam’iyyar APC na jihar, Yusuf Idris ne ya bayyana hakan yayin da yake mayar da martani kan zargin da jam’iyyar PDP ta yi wa APC a wata sanarwa da ya fitar ga manema labarai a Gusau. A cewar sanarwar, zargin da jam'iyyar PDP ta yi wani shiri ne da jam’iyyar ta PDP ke yi ta hanyar amfani da tsohon aminin Gwamna…
