Editor

9513 Posts
Sojoji sun fatattaki ɓarayin ɗanyen man Nijeriya

Sojoji sun fatattaki ɓarayin ɗanyen man Nijeriya

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Rundunar Sojojin Nijeriya a ranar Laraba, ta tabbatar da murƙushe haramtattun matatun mai a Imo da Delta, tare da kama wasu litar man da aka tace ba bisa ƙa'ida ba. Daraktan hulɗa da jama’a na rundunar, birgediya Janar Onyema Nwachukwu, ya tabbatar da hakan a wata sanarwa a ranar Laraba a Abuja. Nwachukwu ya ce, dakarun sojojin na 343 Artillery Regiment, a ranar Litinin ɗin da ta gabata, sun fatattaki wani sansanin ɓarayin mai da ke unguwar Obokofia a Imo yayin da suke gudanar da aikin satar mai. Ya ƙara da cewa, sojojin sun kuma kwato…
Read More
Makamashi: Hada-hadar man fetur kan kawo gurɓatar muhalli da yanayi

Makamashi: Hada-hadar man fetur kan kawo gurɓatar muhalli da yanayi

Tare da BASHIR MUDI YAKASAI Buƙatar a rayu cikin wannan duniya mai cike da ridani, amma cikin sauki da kuma wadata tare da walwala da nishaɗi babu bata lokaci, wato dai rayuwa da suke kira fa 'Aljannar Duniya; inda za su ci duniyar su da tsinke. Wannan gurɓataccen tunani ya sanya dan Adam harkilo dare da rana ta amfani da kyautar da Allah Subuhanahu wata ala ya ba shi daga Basira da Hikima wadanda yake iya amfani da su wajan sarrafa duk wata halitta mai rai da marasa raiharda makamashi da muke batun sa. Makamashin farko da Malam Bahaushe ya…
Read More
Yaƙi da cutar kwalara a Nijeriya

Yaƙi da cutar kwalara a Nijeriya

A cikin rahotonta na baya-bayan nan, Cibiyar Kula da Cututtuka ta Nijeriya ta sanar da jimillar mutane 19,228 da ake zargin sun kamu da cutar kwalara, ciki har da mutuwar mutane 466 a shekarar 2022. A ra'ayin wannan jarida, wannan lamari ne mai firgitarwa da ya kamata gwamnati ta ɗauki matakin daƙile shi cikin gaggawa. Kwalara cuta ce da ake saurin kamuwa da ita, kuma ta na haifar da gudawa da amai. Ana kamuwa da ita daga najasa ta hanyar gurɓataccen abinci, abin sha, da rashin tsafta, kuma ta na haifar da rashin ruwa a jikin ɗan adam. Yawan masu…
Read More
EFCC ta mayar wa wata ‘yar Birtaniya Naira miliyan 25 da aka damfare ta

EFCC ta mayar wa wata ‘yar Birtaniya Naira miliyan 25 da aka damfare ta

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Hukumar da ke Yaƙi da yi wa Tatalin Arzikin Nijeriya Ta'annati EFCC ta mayar wa Christine Brown wata 'yar Birtaniya da aka yi zambata ta intanet, kudinta dala 26,000 kimanin Naira miliyan 25. Mai magana da yawun hukumar ta EFCC Wilson Uwajaren ne ya bayyana haka cikin wata sanarwa da ya fitar a Abuja, yana mai cewa ofishin hukumar reshen jihar Benin ya mayar da kuɗaɗen ranar Litinin. Ya ce Misis Brown ta bayyana jin daɗinta tare da godiya ga hukumar bisa namijin ƙoƙarin da ta yi wajen mayar mata da kuɗaɗenta bayan ta…
Read More
Za a fara kiran waya da na bidiyo a Tuwita ba tare da lamba ba – Musk

Za a fara kiran waya da na bidiyo a Tuwita ba tare da lamba ba – Musk

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Mai kamfanin sada zumunta na X da a baya aka fi sani da Twitter Elon Musk ya ce nan ba da jimawa ba shafin zai bai wa ma'abotansa damar fara kiran waya da na bidiyo. Cikin wani saƙon X da ya wallafa Mista Musk ya ce hakan na daga cikin matakan mayar da shafin na komai-da-ruwanka. “Kiran waya da na bidiyo na nan tafe a shafin X'', kamar yadda ya rubuta ba tare da cikakkken bayani kan lokacin da za a fara amfani da su a shafin ba. Mista Musk ya ce za a…
Read More
Manoman Kano sun fara ganin nasara a gwamnatin Abba – Hajiya Saude Kura

Manoman Kano sun fara ganin nasara a gwamnatin Abba – Hajiya Saude Kura

Daga MUHAMMADU MUJITABA a Kano Sarkin noman mata ta Jihar Kano Hajiya Saude Balarabe Kura, ta ce su a matsayin su na manoma mata wanda aka naɗa ta a Sarkin noman matan jihar Kano sun fara ƙirga riba a zuwan sabuwar gwamnati ta Injiniya Abba Kabir Yusuf, domin a cewarta yadda wannan gwamnatin ta fara tunkarar matsalolin manoma da warware su musamman ta fuskar taki, iri, da samar da tsaro a borane da karkara wannan babbar nasara ce ga manoman Kano maza da mata da ma Nijeriya baki ɗaya. Hajiya Saude Kura ta bayyana haka ne a tsakiyar makon da…
Read More
REB za ta fara samar da wutar lantarki ta zamani a yankunan karkara a Kano

REB za ta fara samar da wutar lantarki ta zamani a yankunan karkara a Kano

Daga MUHAMMADU MUJITABA a Kano Shugaban hukumar samar da wutar lantarki a yankunan karkara ta REB Kano, Injiniya Sani Bala Ilyasu Ɗanbatta MD ya ce yanzu haka wannan hukuma ta yi nisa wajen tsare-tsare da shiri na samar wutar lantarki ta zamani mai aiki da hasken rana domin samar da wadatarciyya wutar lantarki ga al'ummar yankunan karkara da ke jihar Kano. MD Sani Bala ya bayyana haka ne a wani jawabi da ya yi a birnin Kano a ranar Alhamis da ta gabata. Haka kuma ya qara da cewa haɗin kan da kula da gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya…
Read More
Roma da kammala ƙulla yarjejeniyar karvar aron Lukaku daga Chelsea

Roma da kammala ƙulla yarjejeniyar karvar aron Lukaku daga Chelsea

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa ta Roma ta kammala ƙulla yarjejeniyar karɓar aron Romelu Lukaku daga Chelsea wanda zai shafe tsawon kakar bana ya na takawa ƙungiyar mai doka gasar Serie A leda. Roma ƙarƙashin jagorancin Jose Mourinho ta bi sahun manyan ƙungiyoyin Turai da suka miƙa buƙatar karvar aron Lukaku ne bayan da Mauricio Pochettino ya bayyana cewa ɗan wasan baya sahun waɗanda zai yi amfani da su a wannan kaka. Lukaku ɗan Belgium mai shekaru 30 da kanshi ya zabi komawa Roma fiye da Inter Milan ƙungiyar da ya kai wasan ƙarshe na gasar kofin zakarun…
Read More
Kishi da sanin makama ne tushen nasarar Hukumar Alhazan Kano – Kabir Panda

Kishi da sanin makama ne tushen nasarar Hukumar Alhazan Kano – Kabir Panda

Daga MUHAMMADU MUJITABA a Kano Shugaban kula da ayyuka na hukumar jin daɗin alhazan Jihar Kano, Alhaji Kabiru Muhammad Panda ya bayyana cewa kyakkyawan shugabanci mai cike da kishin al'umma da sanin makama da tsoron Allah na Gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf da ya naɗa Alhaji Laminu Rabiu Ɗan Baffa a matsayin shugaban hukumar alhazai da ake cewa goga kasan hanya, shi ne tushen samun kyakkyawan nasara a aikin Hajji da ya gabata a wannan shekara ya sa hukumar jin daɗin alhazai ta jihar Kano ta samu gagarumar nasara na kai alhazai ƙasa mai tsarki su 6567 cikin nasara…
Read More
Juyin mulkin Gabon ya kaɗa hantar shugabannin Afrika

Juyin mulkin Gabon ya kaɗa hantar shugabannin Afrika

•Ba za mu amince da halayyar sojoji ba, inji Shugaban Nijeriya*Shugabannin Kamaru da Rwanda sun sauke manyan hafsoshinsu*Ka daure ka koma Nijar – Tinubu ya roqi Sarkin Musulmi*Hamɓararren Shugaban Gabon ya nemi agaji Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Daga dukkan alamu hamvarar da gwamnatin Ƙasar Gabon ya ɗaga hankalin wasu shugabannin Afrika bisa la’akari da yadda suke ɗaukar matakai daban-daban wajen ganin sun daƙile afkuwar hakan a ƙasashensu, inda ake ganin lamarin a matsayin kaɗuwar hanta. A shekaranjiya Laraba, 30 ga Agusta, 2023, ne sojoji suka hamɓarar da gwamnatin Ƙasar Gabon, makonni bayan kiki-kakar da ake yi da sojojin…
Read More