Editor

9513 Posts
An kashe jami’an kwastom biyu an gudu da bindiga a Kebbi

An kashe jami’an kwastom biyu an gudu da bindiga a Kebbi

Daga JAMIL GULMA a Kebbi Waɗansu da ake kyautata zaton 'yan bindiga ne sun kashe jami'an kwastom guda biyu kuma sun arce da bindiga qirar AK47 guda ɗaya a yayin da su ke sintiri a kan hanyar Ɗakingari zuwa Koko da misalin ƙarfe ɗaya da rabi na daren Alhamis ɗin da ta gabata. Gwamnan jihar Kebbi Malam Nasiru Idris ya nuna rashin jin daɗinsa dangane da wannan ɗanyen aiki jim kaɗan bayan Sallar jana'izar su a harabar asibitin tunawa da Sir Yahaya da ke garin Birnin Kebbi a ranar Alhamis. Malam Idris ya aike da saƙon ta'aziyya ga hukumar kwastom…
Read More
Musawa za ta iya fuskantar ɗauri saboda karya dokar liƙi da Naira

Musawa za ta iya fuskantar ɗauri saboda karya dokar liƙi da Naira

Daga MAHDI M. MUHAMMAD An samu sabon Ministar Fasaha, Al'adu, da Tattalin Arziki tana liƙi da kuɗin Naira. Musawa tana cikin wasu ministoci 44 da aka rantsar a ranar Litinin, 21 ga watan Agusta, 2023, don zama mambobin majalisar ministocin shugaba Bola Ahmed Tinubu. Da yammacin ranar ƙaddamar da bikin, wani hoton bidiyo ya nuna Musawa tana watsawa wata mawaƙiya takardar Naira a wani taron murnar nasarar da ta samu na zama minista. Dokar ta ci karo da sashe na 21 na dokar babban bankin Nijeriya (CBN) na shekarar 2007. Dokar ta CBN ta bayyana cewa yin ta’ammali na liqi…
Read More
Bahaushe da Harshen Hausa

Bahaushe da Harshen Hausa

Daga IBRAHIM HAMISU Ba na nufin na ja ku da nisa wajen doguwar gabatarwa, don gudun gajiyarwa, ba kuma zan yi sassarfa ba, burina ku karanta a natse, duka dai domin ku fahimci wane ne Bahaushe a cikin wannan takaitacciyar maƙalar. To wane ne Bahaushe? Bahaushe shi ne wanda ya ke jin Hausa ya ke magana da Hausa, kuma al'adunsa da ɗabi'unsa duk irin na Hausawa ne. Shi kuwa Farfesa Abdalla Uba Adamu ya bayyana Bahaushe da cewa "Wanda salsalarsa babu wani yaren iyaye sai Hausa, to shi ne Bahaushe. Idan a jerin iyaye da kakanni akwai wanda ba Bahaushe…
Read More
Wike ya bada umarnin kama mamallakin ginin da ya rushe a Abuja bayan ceto mutane 37

Wike ya bada umarnin kama mamallakin ginin da ya rushe a Abuja bayan ceto mutane 37

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja An ceto mutane 37, wasu biyu kuma sun samu raunuka yayin da ake fargabar wasu da dama sun maƙale a lokacin da wani gini ya rufta a titin Legas da ke unguwar Garki a Abuja. Jaridar Blueprint Manhaja ta tattaro cewa Kakakin Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Tarayya (FEMA) Nkechi Isa ta tabbatar da faruwar lamarin da safiyar ranar Alhamis. “Ana ci gaba da aikin ceto yayin da ake ci gaba da neman ƙarin waɗanda abin ya shafa a wurin da ginin ya rufta a titin Legas, a ƙauyen Garki daura da ofishin ‘yan…
Read More
Haɗarin jirgi: Shugaban sojoji ya jajenta wa iyalan jami’an da suka rasu

Haɗarin jirgi: Shugaban sojoji ya jajenta wa iyalan jami’an da suka rasu

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Babban Hafsan Rundunar Sojin Saman Nijeriya, Air Marshal Hasan Abubakar, ya jajenta wa iyalan jami'an jirgin da suka mutu na jirgin sama mai saukar ungulu ƙirar MI-171E da ya yi haɗari a Jihar Neja a ranar 14 ga watan Agustan 2023. Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da rundunar sojin saman Nijeriya, Daraktan hulɗa da jama’a da yaɗa labarai, Air Commodore Edward Gabkwet ya fitar. Da yake jajantawa iyalan, Air Marshal Abubakar ya bayyana cewa, wannan rashin babban koma baya ne ga rundunar sojin saman Nijeriya, wanda zai ɗauki tsawon lokaci kafin hukumar ta farfaɗo.…
Read More
Malagi: Kakakin Nupe kuma kakakin Nijeriya

Malagi: Kakakin Nupe kuma kakakin Nijeriya

Daga NASIR S. GWANGWAZO a Abuja A ranar Litinin, 21 ga Agusta, 2023, ne Shugaban kamfanin gidajen jaridun Blueprint da Manhaja kuma Kakakin Masarautar Nupe, Alhaji Mohammed Idris, wanda ake yi wa laƙabi da Malagi, ya kama aiki a matsayin Ministan Labarai na Tarayyar Nijeriya, inda hakan ke nuni da cewa, baya ga kasancewarsa Kakakin Nupe, a yanzu kuma shine Kakakin Gwamnatin Tarayyar Nijeriya. Wannan ya biyo bayan miƙa sunan Malagi da Shugaban Nijeriya Ahmed Bola Tinubu ya yi ga Majalisar Dattawar Nijeriya, wacce ta tantance Malagin tare da tabbatar da shi a matsayin minista a Nijeriya. Shin wane ne…
Read More
Mu haɗa kai don cigaban Nijeriya – Ministan Labarai

Mu haɗa kai don cigaban Nijeriya – Ministan Labarai

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ministan Yaɗa Labaran Nijeriya, Alhaji Mohammed Idris Malagi, ya yi kira ga ’yan Nijeriya da su haɗa kai su inganta al’amuran ƙasar. A wata sanarwa da mataimakin daraktan yaɗa labarai na ma’aikatar yaɗa labarai ta tarayya, Malam Suleiman Haruna, ya fitar a ranar Talata, ta bayyana cewa ministan ya bayyana hakan ne yayin wata ziyara da Cibiyar Hulɗa da Jama’a ta Nijeriya (NIPR) ta kai masa, inda ministan ya bayyana cewa, aikin sa daga shugaban ƙasa Bola Tinubu shi ne ba da fifiko da sake fasalin qasa don inganta zaman lafiya, haɗin kai, cigaban al'umma. “Wannan…
Read More
Jabun maganin Maleriya ya karaɗe ƙasar nan – Majalisar Tarayya

Jabun maganin Maleriya ya karaɗe ƙasar nan – Majalisar Tarayya

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Kwamitin daƙile yaɗuwar cututtukan ƙanjamau, tarin fuka da zazzaɓin cizon sauro na majalisar wakilai ta ƙasa ta yi kira ga gwamnatin tarayya kan ɗaukar matakan da suka fi dacewa domin hana jabun magungunan cizon sauro a ƙasar nan. Shugaban kwamitin Amobi Ogah mai wakiltan jihar Abia daga jami’yyar LP ya sanar da haka a wata takarda da ya fitar domin tunawa da ranar Cutar zazzaɓin cizon sauro ta duniya da aka yi ranar Lahadi. An keɓe ranar 20 ga Agusta na kowace shekara bayan wani Bature Ronald Ross ya gano cewa macen sauro ‘Anopheline’…
Read More
Gwamnan Kano ya naɗa Fauziyya Suleiman a matsayin mai taimaka masa kan harkokin jinƙai

Gwamnan Kano ya naɗa Fauziyya Suleiman a matsayin mai taimaka masa kan harkokin jinƙai

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnan Jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya naɗa Fauziyya D. Suleiman a matsayin mai taimaka masa kan harkokin jinƙai da mabuƙata. Gwamnan ya tabbatar da naɗin Fauziyya ne a ranar Alhamis yayin wani zama da ya yi da jami'an gwamnatinsa a fadar gwamnatin jihar. Fauziyya D. Suleiman ta yi shura musamman wajen harkokin jinƙai na nema wa mabuƙata da mara sa lafiya tallafi musamman a Arewacin Nijeriya. Naɗin Fauziyya bai zo wa jama'a da mamaki ba, ganin yadda ayyukan gidauniyarta ta Creative Helping Needy Foundation ba ta tsaya iya Kano ba kaɗai, har ma…
Read More
Shugaban Hukumar Ƙwallon Ƙafar Sifaniya ya nemi afuwa bayan sumbatar ‘yar wasa

Shugaban Hukumar Ƙwallon Ƙafar Sifaniya ya nemi afuwa bayan sumbatar ‘yar wasa

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Fira Ministan Spain Pedro Sanchez ya caccaki shugaban Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Ƙasar Sifaniya, Luis Rubiales, kan yadda ya sumbaci 'yar wasan da ta lashe gasar kofin duniya ta mata Jenni Hermoso. A cewar Fira Ministan, bayar da haƙuri kan lamarin kawai ba zai isa ba idan aka yi la'akari da girman abin da ya faru. Shugaban hukumar ƙwallon ƙafar ƙasar Sifaniya, Luis Rubiales ya nemi afuwa sakamakon sumbatar ’yar wasan tawagar ƙwallon ƙafar mata ta ƙasar, Jenni Hermoso da ya yi a leɓe, bayan da suka lashe kofin duniya ta mata da aka kamala a…
Read More