Editor

9513 Posts
Zan ci gaba da raba tallafi har zuwa ƙarshen mulki na, inji Zulum

Zan ci gaba da raba tallafi har zuwa ƙarshen mulki na, inji Zulum

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamna Babagana Zulum na Jihar Borno ya ce gwamnatinsa za ta ci gaba da rabon tallafin kayan abinci ga marasa galihu da kuma al’ummomin da tashin hankali ya shafa iya tsawon mulkinsa. Zulum ya bayyana hakan ne a ranar Talata a Maiduguri yayin da ya ke ƙaddamar da rabon kayan tallafin na Gwamnatin Tarayya ga gidajen dubu 100,000. Zulum ya ce yayin da Gwamnatin Tarayya ta samar da gidaje 100,000, gwamnatinsa na samar da ƙarin gidaje 300,000 don su zama gidaje 400,000. Ya bayyana cewa lamarin Borno ya sha bamban saboda wasu yankunan da…
Read More
Ban goyi bayan yaƙar Nijar ba — El-Rufai

Ban goyi bayan yaƙar Nijar ba — El-Rufai

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya gargaɗi Ƙungiyar Raya Tattalin Arzikin Ƙasashen Yammacin Afirka ECOWAS da ta dakatar da shirin ɗaukar matakin soji a Jamhuriyar Nijar. El-Rufai da ya ke bayyana dalilin da ya sa ya ke jan hankalin ECOWAS da ta yi taka-tsan-tsan, ya ce yan Afirka ‘yan uwan ​​juna ne, kuma yakin da ake yi a kowace ƙasa zai yi illa ga kowa. El-Rufai ya bayyana hakan ne ta wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X, wanda a baya sunansa Tiwita ya bayyana cewa ‘yan ƙasar Nijar da ‘yan…
Read More
Kotun Birtaniya na tuhumar Diezani kan zargin cin hanci

Kotun Birtaniya na tuhumar Diezani kan zargin cin hanci

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Hukumar yaƙi da manyan laifuka a Birtaniya ta tuhumi tsohuwar ministar man fetur ta Nijeriya a kotu, kan laifukan cin hanci. Ana zargin Diezani Alison-Madueke da karɓar cin hancin miliyoyi barkatai na fam ɗin Ingila daga kwangilolin man fetur da iskar gas, da ta bayar don samun cin hanci. Ranar 2 ga watan Oktoba, Diezani Madueke za ta bayyana a gaban Kotun Majistare ta Westminster. Tun bayan kamun da aka yi mata na farko a London cikin watan Oktoban 2015, Diezani Alison-Madueke ta ci gaba da zama a matsayin beli. Jim kaɗan bayan kama…
Read More
Gwamnatin Tinubu za ta fitar da ‘yan ƙasa miliyan 133 daga talauci — Sabuwar Minista

Gwamnatin Tinubu za ta fitar da ‘yan ƙasa miliyan 133 daga talauci — Sabuwar Minista

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Sabuwar ministar harkokin jinƙai da yaƙi da fatara, Dr Betta Edu ta bayyana ƙudirin gwamnatin tarayya na fitar da 'yan Nijeriya miliyan 133 daga ƙangin talauci. Edu ta bayyana hakan ne a lokacin da ta fara aiki a ranar Litinin a Abuja tare da gudanar da taron gaggawa da manyan jami’an ma’aikatun da ke ƙarƙashin ma’aikatar. Ta kuma tabbatar wa 'yan Nijeriya aniyar ta na tabbatar da gaskiya da riƙon amana a zaman ta a matsayin minista. Ta yi bayanin cewa, ma’aikatar za ta cimma burinta ta hanyoyi daban-daban da tsare-tsare da nufin fitar…
Read More
Sharhin wasu baituka na waƙar Ali Makaho mai taken ‘Fahimta’

Sharhin wasu baituka na waƙar Ali Makaho mai taken ‘Fahimta’

Daga BAMAI A. DABUWA KKM Shimfiɗa: Idan ana maganar rubutu ko waƙa ko kuma aka ce maka Adabi a cure, to ba su da iyaka. Kuma komai daidai ne a harkar. Adabi shi ne madubin rayuwar ɗan Adam. Wato ana kallon rayuwar mutum ne da abin da ke kewaye da shi a rubuta ko a rera shi. Ke nan, kamar yadda yake a zahiri mutane suna sata, caca da sauran laifuka, a Adabi ba zunubi ba ne don ka yi ashariya. A sauƙaƙe, idan akwai wasu mutane da aka yi wa uzurin, ƙarya, batsa da saura to marubuta ne da…
Read More
Yadda kyakkyawar zamantakewa ke kawo zaman lafiya

Yadda kyakkyawar zamantakewa ke kawo zaman lafiya

Tare Da ABBA ABUBAKAR YAKUBU A wannan mako ina son hankalin mu ya karkata ne wajen nazarin yadda halayya ta gari da kyautatawa juna a mu'amala ta yau da kullum ke iya haifar da fahimtar juna da zaman lafiya a tsakanin jama'a, musammam mutane masu bambancin ƙabila, addini ko ra'ayin siyasa, da sauran harkoki da zaman tare ke iya haɗa jama'a, daga vangarori daban-daban. Babu shakka zaman lafiya da jama'a, tausayawa, tallafawa, da kaucewa duk wani abu da zai iya kawo saɓani da rashin fahimta a tsakanin mutane, abin a yaba ne matuƙa, babu ma kamar wannan lokaci da jama'a…
Read More
Game da juyin mulkin ƙasar Nijar

Game da juyin mulkin ƙasar Nijar

Daga RAHMA ABDULMAJID A yayin da kwanakin wa'adin ECOWAS ke ƙara ƙaratowa roƙo ɗaya da zan yi wa mahukuntan ECOWAS shi ne, kada su kai hari kan masu juyin mulkin duba da abubuwa uku Na farko dai, mutanen Nijar din sun ji sun gani, don haka a ƙyale su da zavinsu. Na biyu, kuɗaɗe da albarkatu da rayukan da ECOWAS din za ta yi amfani da su wajen kai harin, ta yi amfani da su wajen tsaurara tsaro a bodojinta. Na uku, ƙasashen ECOWAS aminan Rasha ne don haka juyin mulkin Nijar bai kai girman da zai sa waɗannan aasashen…
Read More
Tasirin yin nema kafin a kai ga aure

Tasirin yin nema kafin a kai ga aure

Tare Da AMINA YUSUF ALI Barkanmu da sake haɗuwa a wani makon a shafinmu mai albarka na zamantakewa mai zuwa daga jaridarku mai farin jini, Blueprint Manhaja. A wannan mako muna tafe da dalilan ko na ce tasirin da ya sa ya kamata a fara nema kafin a kai ga aure. Nema dai a aure shi ne zaman da saurayi da budurwa ko bazawara suke yi na soyayya kafin a kai ga aure. Inda saurayi/magidanci zai ta ziyartar budurwa/bazawar (zance), da yi mata waya a kai-a kai har su fahimci juna, sun amince da juna, sannan daga bisani ya turo…
Read More
Buhari ne silar shiga halin da ‘yan Nijeriya suka shiga a yau

Buhari ne silar shiga halin da ‘yan Nijeriya suka shiga a yau

Daga NAFI'U SALISU Al'amarin shugabancin ƙasarmu Nijeriya yana cike da abin al'ajabi da mamaki, game da yadda abubuwa su ke gudana, wanda hakan ya sa a kodayaushe 'yan ƙasar ke buƙatar sauyi. Sai dai halin da ƙasar ke ciki a yanzu, ya zamo sanadin da ya sa 'yan Nijeriya da dama ɗebe tsammani a kan samun salamar da suka daɗe suna fatan samu. Kafin zuwan Buhari da Gwamnatinsa, talakawan Nijeriya suna rayuwa a cikin salama, duk da cewa akwai gurvatattun abubuwa irin su cin hanci da rashawa, halasta kuɗin haram da ayyukan ta'addanci kamar Boko haram. A cikin kashi ɗari,…
Read More
William Tubman: Wanda ya zamanartar da Laberiya

William Tubman: Wanda ya zamanartar da Laberiya

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Laberiya kasa ce ta 'yantattun bayi, wadda aka gina da musguna wa 'yan ƙasar lokacin da aka zavi William Tubman a matsayin shugaban ƙasa. Bayan haɗa kan mutane, ya shirya ƙasar bisa tsarin ci-gaba wanda bai samu ba. An haifi William Vacanarat Shadrach Tubman ranar 29 ga watan Nuwamba 1895. Ya fito daga yankin kudu maso gabashin Laberiya, daga garin da ake kira Harper na gundumar Maryland. Sunan wuraren ya yi kama da na Amurka, saboda Jamhuriyar Laberiya ta ayyana samun 'yanci daga Amirka a shekarar 1947 da 'yantattun bayi suka yi, waɗanda suka dawo daga…
Read More