Editor

9513 Posts
Real Madrid ta fasa sayen Mbappe – Ancelotti

Real Madrid ta fasa sayen Mbappe – Ancelotti

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Kocin Real Madrid, Carlo Ancelotti ya ce, ba zai sayi ɗan wasan gaba Kylian Mbappe daga Paris St-Germain a bana ba. Mbappe, ɗan shekara 24 ya zuwa yanzu ya ƙi rattaba hannu a kan kwantiragi da PSG, lamarin da ya sa ake raɗe-raɗin cewa zai koma ƙungiyar ta La Liga. Ana tunanin cewa PSG a shirye take ta sayar da kyaftin ɗin na Faransa, maimakon yin kasadar rasa shi kyauta idan kwantiraginsa ya ƙare a shekara mai zuwa. Da aka tambaye shi game da yarjejeniyar Mbappe, Ancelotti ya ce "A'a, na yanke hukunci kashi 100." Mbappe…
Read More
Yadda rufe iyaka ya shafi rayuwarmu, cewar al’ummar iyakar Nijeriya da Nijar

Yadda rufe iyaka ya shafi rayuwarmu, cewar al’ummar iyakar Nijeriya da Nijar

Daga Jamil Gulma a Kebbi Babu shakka rufe kan iyakokin da Jamhuriyar Nijar ta yi da Nijeriya ya ƙara rura wuta wajen sanya al'umma a cikin damuwa baya ga irin halin da ake ciki na matsin da rayuwa ta shiga na tsadar rayuwa da rashin abinci, musamman ga ’yan kasuwa da ke kai-komo tsakanin ƙasashen biyu. Wakilin Blueprint Manhaja a Jihar Kebbi ya zagaya waxansu daga garuruwa da ke kan iyakokin Nijeriya da Jamhuriyar Nijar kuma ya zanta da waɗansu mazauna yankunan. Malam Salmanu Abubakar Dole-kaina wani ɗan kasuwa ne da ke sana'ar dabbobi a garin Dole-kaina, wanda ke kusa…
Read More
Ministocin Tinubu zafafa da sanyaya

Ministocin Tinubu zafafa da sanyaya

Tare Da NASIRU ADAMU EL-HIKAYA A ƙarshe dai kamar yadda kowa ya gani a labaru shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya rantsar da ministocin sa 45 da Majalisar Dattawa ta tantance gabanin ta tafi hutu. In za a tuna har ma wataƙila daɗin kammala aikin tantancewar ya sa shugaban majalisar Godwill Akpabio ya ce ya tura ihsani ga dukkanin ’yan majalisar ɗari da tara don su more hutun. A wani yanayi da a ka fahimci an ja hankalin Akpabio cewa ya na jawabi ne kai tsaye da a ke yaɗawa ta kafar talabijin, sai ya waske ko ya gyara zance…
Read More
Shugaban Ƙasar Zimbabwe ya nemi yin tazarce

Shugaban Ƙasar Zimbabwe ya nemi yin tazarce

Shugaban Ƙasar Zimbabwe mai shekaru 80, Emmerson Mnangagwa, ya nuna ra'ayinsa na sake maimara wasu shekaru a kujerar shugabancin ƙasar. Shugaba wanda ya kasance shugaban Ƙasar Zimbabwe na biyu tun bayan dogon mulkin shugaba Robert Mugabe da ya shafe shekaru kusan 40 a mulki. Emmerson Mnangagwa, shi ne tsohon mataimakin shugaban ƙasa Mugabe, ya karɓi ragamar shugabancin ƙasar bayan juyin mulkin, ya kuma yi alƙawarin bunƙasa tattalin arziki ƙasar, da bayar da 'yancin faɗin albarkacin baki, da sassauta takurawar da ake yi wa 'yan adawar da ke magantuwa kan wa'adin mulkin Mugabe, da kuma taɓarɓarewar dangantaka da ƙasashen yammacin duniya.…
Read More
Ƙungiyar AU ta dakatar da Jamhuriyar Nijar daga dukkan sha’aninsu

Ƙungiyar AU ta dakatar da Jamhuriyar Nijar daga dukkan sha’aninsu

Ƙungiyar Tarayyar Afrika, AU, ta fitar da Nijar daga cikinta, tare da umurtar sojojin da suka yi juyin mulki su koma barikinsu don yin abin da aka san su da shi, wato tsare ƙasa. Ƙungiyar ta bayyana hakan ne a wata takarda da ta fitar a ranar Talatar da ta gabata, sannan ta ƙara kira da babbar murya ga sojojin da su saki hamɓararen shugaban ƙasar Mohamed Bazoum. Bayan wannan, ƙungiyar ta AU ta ɗau alwashin sake bibiyar irin matakan da ƙungiyar ECOWAS ta ɗauka kan Jamhuriyar Nijar don ganin ta inda ya kamata ta qara kutsa kai da nufin…
Read More
Lalata da ɗalibai a jami’o’in Nijeriya

Lalata da ɗalibai a jami’o’in Nijeriya

Ga duk mai bibiyar al’amuran da suka shafi shafin yanar gizo, ko kuma in ce harkar yaɗa labarai a qasar nan ya san yadda a ’yan watannin nan ake yawan samun koke-koken game da yadda wani Malaman Jami’o’i ke lalata da ɗalibansu don su ba da maki, ko kuma don a kai su inda ba su kai ba a harkar jarabawa. Ko ba a ce komai ba, wannan wani mummunan abu ne da za a iya cewa bai kama da hakali ba, ko kuma mu ce wani abu ne da ya zama bala’in wanda idan ba a yi hankali ba…
Read More
NPCF ta ayya Muslihu Ali don naɗa shi Ministan Matasa

NPCF ta ayya Muslihu Ali don naɗa shi Ministan Matasa

Ƙungiyar kansiloli ta ƙasa, wato National Progressive Councilor’s Forum (NPCF), ta buƙaci a naɗa shugabanta Hon Muslihu Yusuf Ali a muƙamin Minista a Gwamnatin Tarayya. A cewar ƙungiyar ta ce ta ayyana Muslihu don naɗa shi minista ne biyo bayan sanar da sake Ministan Matasa da Shugaba Bola Tinubu ya yi ba tare da ya bayyana da ko wane ne ba. NPCF ta bayyna haka ne cikin sanarwar manema labarai da ta fitar mai ɗauke da kwanan wata 26 ga Agusta, 2023 da kuma sa hannun Sakataren ƙungiyar na ƙasa, Hon Abayomi kazeem. A cewarta, "La'akari da sanarwar da Fadar…
Read More
Ambaliya: Tinubu zai gina gadar sama a mahaɗar hanyar Abuja zuwa Lokoja

Ambaliya: Tinubu zai gina gadar sama a mahaɗar hanyar Abuja zuwa Lokoja

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Gwamnatin Tarayya ƙarƙashin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ta bayyana shirin gina gadar sama a kan hanyar Abuja zuwa Lokoja domin daƙile matsalar ambaliyar ruwa. Ministan ayyuka, David Umahi ya bayyana haka ne a ranar Talata, 22 ga watan Agusta, 2023, a rangadin da ya ke yi na duba ayyukan gina hanyar Abuja zuwa Lokoja, kwana guda bayan ƙaddamar da shi minista. Ministan tare da gwamnan jihar Kogi Yahaya Bello da wasu daraktoci a ma’aikatar sun ziyarci wasu wuraren aiki a kan hanyar. A cewar ministan, hanyar Abuja zuwa Lokoja wata babbar ƙofa ce da ta…
Read More
Sanata Lawan ya tallafa wa al’ummar mazaɓarsa da shinkafa da gero

Sanata Lawan ya tallafa wa al’ummar mazaɓarsa da shinkafa da gero

Daga MUHAMMAD AL-AMEEN a Damaturu Tsohon Shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya, Sanata mai wakiltar Yobe ta Arewa, Dr. Ahmad Lawan, ya tallafa wa al'ummar mazaɓarsa da kayan abinci kimanin buhuna 9000 na hatsi da shinkafa don rage raɗaɗin tsadar rayuwa a yankin. Wannan matakin tallafin na Sanata Lawan, daɗi ne a kan makamancin sa wanda Gwamnatin Tarayya da ta Jihar Yobe suka ɗauka wajen rage wa al'umma wahalhalun da suke fuskanta sakamakon cire tallafin man fetur. Sanata Ahmad ya ƙaddamar da tallafin kayan abincin, wanda Gidauniyar 'SAIL' ta ɗauki nauyin aiwatar da shi a cikin gundumomi 60 da ke Yobe ta…
Read More
EFCC da CCB sun gayyaci Muhuyi Rimingado don amsa tambayoyi

EFCC da CCB sun gayyaci Muhuyi Rimingado don amsa tambayoyi

Daga BASHIR ISAH Hukumar yaƙi da rashawa EFCC da takwararta ta kyautata ɗa'ar ma'aikata, CCB, sun gayyaci Shugaban Hukumar Sauraren Ƙorafe-ƙirafe da Yaƙi da Rashawa na Jihar Kano (PCACC), Muhuyi Rimingado, don amsa tambayoyi kan batun kuɗaɗen hukumar. A baya-bayan nan aka ji Rimingado na cewa yana gudanar da bincike kan faifan bidiyo da aka yaɗa mai alaƙa da tsohon Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Ganduje mai nasaba da cin hanci Dala. Ganduje ya samu umarnin kariyar da ta hana hukumar yaƙi da rashawa ta bincike shi da iyalinsa da dukkan masu riƙe da muƙaman siyasa a ƙarƙashinsa. Sai dai kuma…
Read More