Editor

9513 Posts
Ƙasashen Turai da man fetur a Nahiyar Afirka

Ƙasashen Turai da man fetur a Nahiyar Afirka

Daga BASHIR MUDI YAKASAI Masana tarihi sun tabbatar da dalilan da suka sa ƙasashen Turai suka kasa barin Nahiyar Afirka duk da cewa sun ba su ’yancin kai, sama da shekaru 60 da suka shuɗe. Duk da cewa sun kwashe sama da shekaru 100, suna waɗari a Afirka suna wawason bayi da amfanin gona tun daga dawa, alkama, auduga da sha’ir da ma’adanai irin su zinare da murjani da azurfa da hauran giwa da jimina da gashinta da kuma turaren wuta. Da tafiya ta yi tafiya, aka gano Ɗanyen man fetur da gas da kuma dangoginsa, Turawan Yamma da na…
Read More
Dubun wani tsohon soja mai yi wa Boko Haram safarar makamai ta cika a Bauchi

Dubun wani tsohon soja mai yi wa Boko Haram safarar makamai ta cika a Bauchi

Daga BASHIR ISAH Rundunar Sojin Nijeriya ta bayyana cewar, jami'anta sun kama wani tsohon soja da ake zargi da yi wa Boko Haram safarar makamai a Jihar Bauchi. Cikin bayanan da ta fitar a ranar Juma'a, rundunar ta ce, “A ranar 18 ga Yuli, 23, jami'anta sun cafke wani da ake zargi mai safarar makamai ne a Boi cikin yankin Ƙaramar Hukumar Bogoro a Jihar Bauchi. “Binciken farko ya gano wanda ake zargin korarren soja ne a Damasak. Askarawa sun gano ƙananan bindiga 2, bindiga ƙirar magazine 2 da kuma alburusai," in ji rundunar. Kazalika, rundunar ta ce ta sake…
Read More
Gwamna Lawan ya karrama mahajjaciyar da ta mayar da tsuntuwar Dala 80,000 a Saudiyya

Gwamna Lawan ya karrama mahajjaciyar da ta mayar da tsuntuwar Dala 80,000 a Saudiyya

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawan, a ranar Alhamis, ya karrama hajiyar da ta mayar wa mwanda ya jefar da Dala 80,000 a wajen aikin Hajjin da ya gabata a ƙasar Saudiyya. Mahajjaciyar, Hajiya Aishatu 'yar Guru Nahuce daga Ƙaramar Hukumar Bungudu ta jihar Zamfara ta tsinci Dala 80,000 (N64,240,000) sannan ta miƙa su ga jami'in hukumar jin daɗin alhazai ta Zamfara domin mayar wa ga mai shi. A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta ce gwamnan ya karrama mahajjaciyar ne tare da dukkan sarakunan jihar,…
Read More
Hukumar CAC ta yi taron wayar da kan hukumomin tsaro da masu kamfanoni a Kano

Hukumar CAC ta yi taron wayar da kan hukumomin tsaro da masu kamfanoni a Kano

Daga IBRAHIM MUHAMMAD a Kano Hukumar Yi wa Kamfanoni Rijista ta Ƙasa ta yi taro na wayar da kan jami'an tsaro, hukumomi masu yaƙi da cin hanci da rashawa da sauran ƙungiyoyi masu zaman kansu. Taron wanda aka gudanar a Jihar Kano ya samu halartar shugaban hukumar ta ƙasa Garba Abubakar da sauran masu ruwa da tsaki na hukumar da 'yan kasuwa wakiilan jami'an tsaro da ƙungiyoyi. Da yake zantawa da manema labarai shugaban hukumar ta CAC na ƙasa Garba Abubakar ya ce taron na wayar da kan jami'ai ne da ƙungiyoyi da masu zuba hannun jari da masu gudanar…
Read More
Kotu ta kori ƙarar DSS na neman a ci gaba da tsare Emefiele

Kotu ta kori ƙarar DSS na neman a ci gaba da tsare Emefiele

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Wata Babbar Kotun Tarayya da ke zamanta a Abuja ta yi watsi da buƙatar da hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ta shigar na neman a tsawaita tsare Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Godwin Emefiele. Hukumar DSS ta shigar da ƙarar ne a ranar Laraba, 25 ga watan Yuli, 2023, inda ta ce ta gano wasu sabbin hujjoji kan Emefiele. Sai dai kotun ta yi watsi da buƙatar, saboda rashin hurumi. Mai shari’a Hamza Muazu ya ce kotun majistare, ba babbar kotun ba, tana da haƙƙi na musamman na bayar da umarnin tsare mutane…
Read More
An zargi Shugabar Hukumar FCC da sayar da guraben aiki a ma’aikatun Gwamnatin Tarayya

An zargi Shugabar Hukumar FCC da sayar da guraben aiki a ma’aikatun Gwamnatin Tarayya

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Kwamishinonin Hukumar (FCC) sun zargi shugabar hukumar Farida Dankaka da “sayar da guraben ayyukan yi” a ma’aikatu da hukumomin tarayya (MDAs). Kwamishinonin sun yi wannan zargin ne a lokacin da kwamitin wucin gadi na Majalisar Wakilai ke binciken MDAs da jami’an tsaro da manyan makarantu kan badaƙalar ayyukan yi a Abuja. Kwamishinonin FCC da suka yi zargin sun haɗa da Abdulrasaq Adeoye (Osun), James Dan’iya (Kwara), Abdulwasiu Bawan-Allah (Lagos), Moses Anaughe (Delta), Mamman Alakayi (Nasarawa), da dai sauransu. Kwamishinonin sun kuma yi zargin cewa Madam Ɗankaka ta haxa baki da Hukumar Yaƙi da yi…
Read More
Gwamna Lawan ya jaddada aniyar magance ƙarancin ruwa a Zamfara

Gwamna Lawan ya jaddada aniyar magance ƙarancin ruwa a Zamfara

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamna Dauda Lawal, a ranar Laraba, ya karɓi rahoton wucin gadi daga kwamitin ba da shawara kan farfaɗo da ruwan sha na jihar Zamfara, yana mai jaddada ƙudirin gwamnatinsa na samar wa babban birnin jihar da sauran ƙananan hukumomin jihar da tsaftataccen ruwamai ɗorewa. Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa Gwamna Lawal ya tabbatar da hakan ne a lokacin da yake karvar rahoton a zauren majalisar da ke gidan gwamnati da ke Gusau. Gwamnan ya yaba wa tawagar bisa hidimar da suke yi wa…
Read More
Gwamnatin Tinubu ta gano ma’aikata 1,618 da takardun aikin bogi

Gwamnatin Tinubu ta gano ma’aikata 1,618 da takardun aikin bogi

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnatin Tarayya ƙarƙashin jagorancin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta gano wasu ma’aikatan gwamnati 1,618 da takardun aikin bogi a ƙoƙarinta na daqile badaƙala da kutsawa cikin ma’aikatan gwamnati ba tare da katsewa ba. Shugabar ma’aikata ta tarayya, Folashade Yemi-Esan ce ta bayyana hakan a ranar Talata, yayin da take magana yayin wani taron manema labarai gabanin makon ma’aikatan gwamnati na 2023. Ta ce an gano hakan ne bayan ɓullo da hanyoyin da hukumar ta kafa domin magance kura-kuran da aka gano a cikin tsarin hada-hadar ma’aikata da tsarin biyan albashi (IPPIS). A cewar shugaban…
Read More
Za mu samar da sababbin hanyoyin magance barazanar tsaro – Janar Musa

Za mu samar da sababbin hanyoyin magance barazanar tsaro – Janar Musa

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Babban Hafsan Tsaro na Ƙasa (CDS), Manjo Janar Christopher Gwabin Musa, a ranar Alhamis, ya yi kira da a samar da sababbin hanyoyin magance matsalolin tsaro da ke kunno kai a faɗin ƙasar nan. Musa ya yi wannan kiran ne a Abuja, yayin da yake bayyana ra’ayinsa na shugabancin rundunar sojin Nijeriya. A cikin wata sanarwa da shi da kansa ya sanya wa hannu, Musa ta ce, ɗimbin ƙalubalen tsaro da ke cigaba da taɓarɓarewa a ƙasar, Nijeriya na kira da a ɗauki ƙarin matakai domin daƙile su. Bisa la'akari da haka, Musa ya bayyana cewa,…
Read More
Gwamnatin Ingila ta ƙwace ɗan likitan Nijeriya saboda ya zane shi

Gwamnatin Ingila ta ƙwace ɗan likitan Nijeriya saboda ya zane shi

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Wani likitan ɗan Nijeriya da ke ƙasar Birtaniya ya rasa damar sa hannun gwamnati na cigana da riƙe ɗansa mai shekaru 16 bayan ya yi masa bulala. Wata mai fafutukar kare haƙƙin yara da aka fi sani da Pepstalk1 ta bayyana hakan a shafinta na Instagram ranar Laraba. Ta bayyana cewa, likitan ɗan Nijeriya ya yi wa ɗan nasa bulala bayan ya kama shi da abokansa suna kallon wani faifan bidiyo da bai dace ba. An ruwaito abokansa sun sanar da ’yan sanda kuma suka gaya musu cewa a lokacin da uban yake dukan ɗansa da…
Read More