28
Jul
Daga BASHIR ISAH Majalisar Dattawa ta ce ya zuwa ranar Litinin mai zuwa za ta fara tantance sunayen mutum 28 da Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya aike mata wanda yake neman naɗa su muƙaman ministoci. Mai magana da yawun Majalisar, Sanata Adeyemi Adaramodu (APC-Ekiti), shi ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai ranar Alhamis a Majalisar ta Dattawa. Adaramodu ya ce duk da dai Litinin ba ranar zaman majalisar ba ce, amma la'akari da muhimmancin da ke tattare da aikin "ya sa muka dakatar da dokokinmu domin fara aikin tantancewar Litini mai zuwa." Ya ƙara…
