Editor

9513 Posts
Abin damuwa ne halin ƙuncin da zawarawa ke ciki – Sayyida Aisha

Abin damuwa ne halin ƙuncin da zawarawa ke ciki – Sayyida Aisha

"Matsalar aure da na shiga ta sa ni kafa ƙungiyar taimakawa mata" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Masu hikimar magana na cewa, ciwon 'ya mace na ’ya mace ne. Kuma abu namu maganin a kwaɓe mu. Wannan duk maganganu ne na azanci da ake jingina su ga mata. Duk kuwa da cewa da ake yi mata ba su cika son junansu ba, ko nuna goyon gaba da tausayawa 'yan uwansu mata ba. Amma wannan zargin bai cika zama gaskiya ba, domin kuwa ana samun mata da ke nuna tsananin tausayawa da tallafawa ga 'yan uwan su, sakamakon wata jarabawar rayuwa da…
Read More
Tinubu ya yi gargaɗi kan yunƙurin juyin mulki a Nijar

Tinubu ya yi gargaɗi kan yunƙurin juyin mulki a Nijar

Daga BASHIR ISAH Shugaban Nijeriya kuma Shugaban Ƙungiyar Raya Tattalin Arzikin Ƙasashen Yammacin Afirka (ECOWAS), Bola Ahmed Tinubu, ya yi gargaɗin cewa ECOWAS ba za ta yarda da duk wani al'amari da zai haifar da cikas ga zaɓaɓɓiyar gwamnati a yammacin Afirka ba. Tinubu ya yi wannan gargaɗi ne a matsayin martani kan fargabar yiwuwar juyin mulki a Jamhuriyar Nijar inda sojojin ƙasar suka tsare Shugaban Ƙasar, Mohamed Bazoum. Ya yi gargaɗin ne a matsayinsa na shugaban ECOWAS, cikin sanarwar da ya fitar a ranar Laraba, inda ya bayyana datse fadar shugaban ƙasar Nijar da sojojin suka yi a matsayin…
Read More
‘Yar boko kake aure?

‘Yar boko kake aure?

Daga AMINA YUSUF ALI 'Yar boko! Wannan shi ne sunan da ake kiran macen da ta yi karatu kuma take yin aiki ko take karatun gaba da Sakandare, ko ta gama, ko tana aikin albashi ko ma ba ta aikin. Wannan shi ne lissafin kuɗin goro da ke wa mace 'yar boko a ƙasar Hausa. Masu karatu barkanmu da haɗuwa a wani makon mai albarka! Ta cikin jaridarku mai farin jini, Manhaja. A yanzu kuma za mu tsunduma kan maudu'inmu na wannan mako. A kan auren 'yar boko da irin abubuwan da suke tattare da auren. Duba da yadda a…
Read More
Likitoci sun tsunduma yajin aiki

Likitoci sun tsunduma yajin aiki

Daga BASHIR ISAH Ƙungiyar Likitocin Nijeriya (NARD) ta fara yajin aiki a wannan Laraba. Shugaban ƙungiyar, Dr Emeka Orji, shi ne ya bayyana haka ga majiyarmu ranar Talata, inda ya ce likitoci za su tsunduma yajin aiki ranar Laraba, 26 ga Yuli, 2023 da misalin ƙarfe 12 na tsakar dare. Orji ya ce, sun cim ma matsayar shiga yajin aikin ne a wajen taron shugabannin ƙungiyar da ya gudana cikin Yuli a Legas. Ƙungiyar ta ce mabobinta sun shiga yajin aikin ne domin cim ma buƙatunsu a wajen gwamnati. Ta ce buƙatun mambobin nata sun haɗa da neman a biya…
Read More

Yunƙurin juyin mulki: Fadar Shugaban Ƙasar Nijar ta yi ƙarin haske

Fadar Shugaban Ƙasar Jamhuriyar Nijar ta fitar da sanarwa dangane da halin da ake ciki na fargabar yiwuwar shirin juyin mulki a ƙasar inda ta tabbatar da cewa lallai an samu wasu sojoji da ke tsaron fadar shugaban ƙasar da suka ɗauki matakin da ya saɓa wa doka. A cewar sanarwar, sojojin da suka yi wannan yunƙuri ba su samu haɗin kan takwarorinsu da ke tsaron fadar ba, kuma a halin da ake ciki Shugaba Bazoum Mohamed da iyalinsa na cikin ƙoshin lafiya. Rundunar sojin Nijar ta ce a shirye take ta ɗauki matakin murƙushe dukkanin waɗanda suke da hannu…
Read More
‘Yan bindiga sun kashe farar hula 26, sojoji 7 a Zamfara

‘Yan bindiga sun kashe farar hula 26, sojoji 7 a Zamfara

Daga SANUSI MUHAMMAD, a Gusau Aƙalla mutane 26 ne wasu ‘yan bindiga suka kashe tare da wasu sojoji bakwai a ƙauyen Kangon Garacci da ke ƙarƙashin gundumar Ɗangulbi a ƙaramar hukumar Maru a Jihar Zamfara. Wani Mazaunin yankin mai suna Malam Bello Ɗangulbi, shi ne ya bayyana haka a wata tattaunawa da Blueprint Manhaja ta yi da shi ta waya a ranar Talata. A cewarsa, ‘yan bindigar sun mamaye al’ummar ne da misalin karfe 04:00 na yammacin ranar Litinin. Ya ce, ‘yan bindigar da ke ƙarƙashin ƙasurgumin ɗan ta'addan nan da ya addabi yankin da aka fi sani da Ali…
Read More
DSS ta sake tsare Emefiele jim kaɗan bayan Kotu ta ba da belinsa

DSS ta sake tsare Emefiele jim kaɗan bayan Kotu ta ba da belinsa

Daga BASHIR ISAH Jami'an DSS sun dake tsare dakataccen Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Godwin Emefiele, bayan rikita-rikuta da jami'an kula da gidan gyaran hali. Manjaha ta tattaro cewar an sake tsare Emefiele ne jim kadan bayan da Babbar Kotun Tarayya a Legas ƙarƙashin jagorancin Alƙali Nicholas Oweibo ta ba da belinsa kan Naira miliyan 20. Yayin zaman Kotun a ranar Talata Alƙali Oweibo ya ba da umarnin a tsare Emefiele a kurkuku har sai ya cika sharuɗɗan belin da aka gindaya masa. Jim kaɗan bayan hukuncin ne sai jami'an DSS suka shirya kansu a wajen kotun inda suka sake…
Read More
Hisbah ta cafke waɗanda ake zargi da yunƙurin auren jinsi a Kano

Hisbah ta cafke waɗanda ake zargi da yunƙurin auren jinsi a Kano

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Hukumar Hisba ta Jihar Kano ƙarƙashin jagorancin Sheikh Aminu Daurawa, ta ce ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da yunƙurin shirya auren jinsi a jihar. Rahotanni sun nuna cewa Kwamandan Hisbah, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a ranar Asabar. Ya bayyana a wani faifan bidiyo cewa an ga wasu samari biyu masu suna Khalifa da Abubakar suna ƙoƙarin sumbatar juna a yayin wani biki, wanda ake zargin bikin aurensu ne. Sai dai waɗanda ake zargin sun musanta zargin, inda suka ce taron…
Read More
Kotu ta ba da belin Emefiele

Kotu ta ba da belin Emefiele

Daga BASHIR ISAH Babbar Kotun Tarayya da ke Legas ta ba da belin dakataccen Geamnan Babban Bankin Nijeriya, CBN, Godwin Emefiele kan kuɗi Naira miliyan 20 da shaida guda. Mai Shari'a Nicholas Oweibo ne ya ba da belin bayan da lauyan Emefiele, Joseph Daudu (SAN) ya shigar da buƙatar belin ga kotun. Alaƙalin ya yi watsi ƙorafin Gwamnatin Tarayya kan Emefiele saboda rashin kare ƙorafin nata da hujjoji. Kazalika, Emefiele ya ƙi amincewa da tuhumar da ake yi masa kan aiakata laifuka biyu da suka haɗa da mallakar bindiga da alburusai ta harantacciyar hanya. An ba da belin Emefiele ɗin…
Read More
Adamu Ɗan Maraya Jos

Adamu Ɗan Maraya Jos

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ɗan Maraya Jos (an haife shi Adamu Wayya, 20 Disamba 1946 – 20 Yuni 2015) fitaccen mawaƙin Hausa ne daga Jos, Nijeriya. Ya shahara da salon waƙoƙinsa na musamman wanda ya haɗa waƙoƙin Hausa da jigogi da kayan kiɗa na zamani. An haifi Ɗan Maraya Jos a Sabon Gari, al’ummar Hausawa da suka fi yawa a garin Jos na Jihar Filato a Nijeriya. Ya girma a cikin gida na kiɗa kuma ya fara yin wasa tun yana ƙarami. Kakansa ne ya zaburar da shi, wanda ya kasance mawaƙin gargajiya na Hausa, ya kuma koyi yin kiɗa…
Read More