Editor

9513 Posts
An gurfanar da Emefiele kan zargin mallakar bindiga ta haramtacciyar hanya

An gurfanar da Emefiele kan zargin mallakar bindiga ta haramtacciyar hanya

Daga BASHIR ISAH An gurfanar da dakataccen Shugaban Babban Bankin Nijeriya (CBN), Godwin Emefiele, a Babbar Kotun Tarayya da ke Ikoyi a Legas bisa zargin laifuka biyu da suka haɗa da mallakar bindiga da alburusai ba bisa ƙa'ida ba. Majiyarmu ta ce jami'an DSS ne suka shigo da Emefiele ɗin kotun da safiyar ranar Talata. Zaman kotun ya gudana ne ƙarƙashin jagorancin Mai Shari'a Nicholas Oweibo. Tsohon Shugaban Ƙungiyar Lauyoyin Nijeriya (NBA), Joseph Daudu, shi ne ya jagoranci tawagar lauyoyin da ke kare Emefiele ɗin. Kodayake dai Emefiele ya musanta tuhumar da ake yi masa, inda ya ce bai aikata…
Read More
Babu gudu ba ja da baya game da janye ‘yan sanda masu gadin shafaffu da mai – Runduna

Babu gudu ba ja da baya game da janye ‘yan sanda masu gadin shafaffu da mai – Runduna

Daga BASHIR ISAH Rundunar 'Yan Sanda ta Nijeriya ta ce babu abin da zai sa ta janye matakin da ta ɗauka na janye jami'anta daga bai wa masu ƙumbar susa (VIPs) a ƙasar. Wannan na zuwa ne bayan mako guda da rundunar ta ƙaryata janye jami'an kwantar da tarzoma daga bai wa shafaffu da man kariya cikin wata takardar sirri da ta fito fili. Bayan ce-ce-ku-ce kan ƙaryata batun da rundunar ta yi, wasu 'yan ƙasa na ra'ayin 'yan sandan ba su da niyar aiwatar da tsarin. Sai dai, da yake maida martani kan batun cikin sanarwar da ya fitar…
Read More
Sheikh Dakta Yusuf Ali (Sarkin Malaman Gaya)

Sheikh Dakta Yusuf Ali (Sarkin Malaman Gaya)

An haife shi a cikin garin Gaya ta Jihar Kano a shekarar 1950. Ya haddace Alƙur'ani ya na da shekara 11, ya gama duk wani fanni na ilimi da ake karantawa a makarantun soro (ƙarshen ilimi kenan a wancan lokacin) yana da shekaru 15. Ya fara rubutun Alkur'ani yana da shekaru 13, ya zama Alaramma mai darasu tun ina da shekaru 14.Tsangayar sa tana nan a halin yanzu a Gashua, a Katuzu/Garin Yamma, jihar Yobe. Malam Musa Dan Dikkware shi ne Halifa sa mai darasu a halin yanzu. Ya fara shimfiɗa buzu na karantar da ɗalibai a makarantar soro tun…
Read More
Wata mai koyon sana’a ta sace yaron uwargijiyarta a Neja

Wata mai koyon sana’a ta sace yaron uwargijiyarta a Neja

Daga BASHIR ISAH Bayanai daga Jihar Neja sun wata mai koyon sana'ar gyaran suma ta sace yaron matar da take koyon sana'ar a wajenta a shagonta da ke babbar kasuwar Minna, babban birnin jihar. Majiyarmu ta ce yaron dablamarin ya shafa, Chinedu Chukwueke, watansa shida da haihuwa. Mahaifin yaron, Chikezie Stanley Chuks, shi ne ya bayyana mummunan labarin a shafinsa na Facebook. Inda ya ce, “Barka da rana, an ɗauke mini yarona ɗan wata shida da haihuwa mai suna Chinedu Chukwueke a shagon matata yau Lahadi, 23 ga Yuli, 2023 a kasuwa Kure, Minna. "Idan aka samu muhimman bayanai game…
Read More
Har yanzu ‘yan Nijeriya na fama da matsalar tsaro lokacin Tinibu – Dauda

Har yanzu ‘yan Nijeriya na fama da matsalar tsaro lokacin Tinibu – Dauda

Daga AMINU AMANAWA a Sakkwato Ƙasa da watanni biyu da soma mulkin Shugaban Ƙasa Bola Ahmad Tinibu al’umma na cigaba da bayyana damuwarsu kan kamun ludayin gwamnatin musamman a ɓangaren tsaro. A cewar galibin waɗanda Jaridar Manhaja ta zanta da su sun bayyana damuwar su, kan yadda duk da alƙawurran da gwamnatin Tinibun ta yi wa ‘yan ƙasa kan lamarin tsaro, al’umma ke cigaba da ɗanɗana kuɗar su sakamakon har-haren ‘yan bindiga musamman ma a jihohin Arewa maso Yammacin Nijeriya. Kwamared Bishir Dauda Sabon Unguwa Katsina, shi ne Babban Magatakardan Ƙungiyar Muryar Talaka a Nijeriya, a zantawar da wakilinmu a…
Read More
An kama ɗan bindiga da ake zargi da yunƙurin kai hari gidan Atiku a Adamawa

An kama ɗan bindiga da ake zargi da yunƙurin kai hari gidan Atiku a Adamawa

Daga BASHIR ISAH Bayanai daga Jihar Adamawa sun ce an damƙe wani da ake zargin ɗan Boko Haram bayan da ya yi yunƙuri kai harin bom a gidan toshon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, da ke Yola, babban birnin jihar. An ce an kama wanda ake zargin, Jubrila Mohammed ne a ranar Lahadi bayan da aka lura da take-takensa. Mohammed ya faɗa wa 'yan sanda cewa, da shi aka shirya yadda za a kai harin bom a gidan Atiku da wani ɓangare na American University of Nigeria da kuma Babban Masallacin Modibbo Adama duk a Yola. Majiyarmu ta ce yanzu…
Read More
Ana gallaza wa ɗalibai Musulmai a jami’o’i mallakin Kiristoci a Nijeriya – MURIC

Ana gallaza wa ɗalibai Musulmai a jami’o’i mallakin Kiristoci a Nijeriya – MURIC

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ƙungiyar Kare Muradun Musulmai a Nijeriya (MURIC) ta yi zargin ana gallaza wa ɗalibai Musulman da ke karatu a jami’o’i musu zaman kansu mallakin Kiristoci a ƙasar nan. Ƙungiyar ta faɗi hakan ne a cikin wata sanarwa wacce Shugabanta, Farfesa Ishaq Akintola ya sa wa hannu, ta kuma fitar a ranar Alhamis. A cikin sanarwar, MURIC ta zargi jami’o’in da nuna gaba da tsana da kuma tsangwama ga Musulmi da kuma adddinin Musulunci ta hanyar yadda ake tirsasa xalibai Musulmai zuwa Coci da kuma hana su sa hijabi da sauransu. “Mun samu rahotanni da yawa kan…
Read More
Tsadar fetur: COEASU ta umarci malamai su koma aiki sau biyu a mako

Tsadar fetur: COEASU ta umarci malamai su koma aiki sau biyu a mako

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ƙungiyar Malaman Kwalejin Ilimi ta Ƙasa (COEASU) ta bai wa mambobinta umarnin taƙaita zuwa aiki zuwa sau biyu a sati har sai gwamnatin Tarayya ta ƙara musu albashi da kashi 200. Ƙungiyar ta ce, umarnin zai fara aiki ne nan take har zuwa lokacin da za ta gudanar da taron gaggawa domin yanke adadin kwanakin da ya kamata malaman su cigaba da zuwa aiki. Shugaban ƙungiyar, Dokta Smart Olugbeko ne ya bayyana hakan yayin ganawa da manema labarai a Abuja, inda ya ce duk da cewa ƙarin kuɗin man fetur da gidajen mai suka yi a…
Read More
Ƙungiyar Hisbah a Katsina ta yi taron shekara

Ƙungiyar Hisbah a Katsina ta yi taron shekara

Daga RABIU SANUSI a Kano Hukumar Hisba ta Ƙasa, reshen Jihar Katsina ƙarƙashin jagorancin Muhammad Rabiu Garba, ta gudanar da taron shugabanni karo na farko. Hakan dai na ƙunshe ne a cikin wata takardar da aka fiddo bayan taro da sakataren ƙungiyar ACH. Muhammad Aminu Bello ya sawa hannu ya raba wa manema labarai a jihar. A cewar sanarwar taron ya samu halartar kananan hukumomi talatin cikin talatin da huɗu da ke akwai a jihar. Sanarwar ta ƙara da cewa, kwamandojin waɗannan ƙananan hukumomi talatin sun jaddada mubaya’a ga kwamanda na Jiha CH. Muhammad Rabi’u Garba. Taron ya samu halarcin…
Read More
Sanatan Kano ta Tsakiya: Kotu ta tabbatar da nasarar Hanga

Sanatan Kano ta Tsakiya: Kotu ta tabbatar da nasarar Hanga

Daga BASHIR ISAH Kotun sauraren ƙararrakin zaɓe mai zamanta a Kano, ta tabbatar da sanar da Sanata Rufa’i Hanga ya samu a zaɓen da ya gabata a matsayin mai wakiltar Kano ta Tsakiya a Majalisar Dattawa. Majiyarmu ta ruwaito cewa ɗan takarar Jam'iyyar APC na sanatan Kano ta Tsakiya a zaɓen da aka gudanar 25 ga Fabrairun da ya gabata, Abdulsalam Abdulkarim Zaura, shi ne ya shigar da ƙara kotu inda ya ƙalubalanci ayyana ɗan takarar jam'iyyar NNPP, Rufa'i Hanga, da hukumar zaɓe INEC ta yi a matsayin wanda ya lashe zaɓen. Zaura, ta hannun lauyansa, Ishaka Dikko (SAN), ya…
Read More