Editor

9513 Posts
Tsadar litar fetur: Ba a rabu da Bukar ba…

Tsadar litar fetur: Ba a rabu da Bukar ba…

Daga NASIRU ADAMU EL-HIKAYA Tun janye tallafin man fetur da shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu a jawabin sa karɓar mulki ranar 29 ga watan Mayu a ka shiga ganin sauye-sauye ta fuskar tattalin arziki da kusan dukkan lamuran da su ka shafi rayuwar yau da kullum. Masu sharhi ma sun yi ta bayanin ainihin abun da ya faru na tashin farashin nan take tun gabanin aƙalla watan jiya na Yuni da a ka yi bayanin sai watan ya kare ne tallafin da a ka ciren zai kammala wato a wannan watan a Yuli sai a buɗe sabon babi na rayuwa…
Read More
Juyin mulkin Nijar: Bazoum ya sha alwashin gwagwarmayar kare dimukraɗiyya

Juyin mulkin Nijar: Bazoum ya sha alwashin gwagwarmayar kare dimukraɗiyya

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Muhammad Bazoum, Shugaban Ƙasar Nijar, wanda sojoji suka yi wa juyin mulki a ranar Laraba, ya ce, ya sha alwashin kare ribar dimokraɗiyya da suka sha yin gwagwarmaya a kai wajen nema wa al'ummar ƙasar 'yanci. Rahotanni sun ce, Mohamed Bazoum na tsare a hannun waɗanda suka shirya maƙarƙashiyar yi masa juyin mulki, waɗanda tun farko suka sanar da dakatar da duk wasu cibiyoyin gwamnati a ƙasar. Ita ma rundunar sojojin Nijar ta yi watsi da juyin mulkin da aka yi wa shugaban ƙasar. Babban hafsan sojin qasar ya ce, yana buƙatar "kiyaye mutuncin…
Read More
Tinubu ya naɗa Malagi, El-Rufai, Wike muƙamin minista

Tinubu ya naɗa Malagi, El-Rufai, Wike muƙamin minista

*An kasa samun matsaya kan ministocin Kano, Zamfara da Kebbi Daga MAHDI M. MUHAMMAD A ƙarshe dai Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya aike da sunayen mutane 28 da ya zaɓa a matsayin ministoci, domin naɗa su a matsayin mabobin Majalizar Zartarwar Tarayyar Nijeriya. Bayan an daɗe ana jiran jerin sunayen ne a jiya Alhamis Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya zo zauren majalisar da ƙarfe 12:05 na rana, inda bayan an yi addu’ar buɗe zaman zauren sai kuma ya bayyana cewa, majalisar za ta shiga wani zama na musamman. Bayan zaman ne ya fito ya bayyana jerin sunayen…
Read More
Gwamnati za ta soke wasu manhajojin ba da rance saboda cuzguna wa ‘yan Nijeriya

Gwamnati za ta soke wasu manhajojin ba da rance saboda cuzguna wa ‘yan Nijeriya

Daga AMINA YUSUF ALI Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta ce za ta soke manhajojin ba da rance gida biyu saboda suna cuzguna wa 'yan Nijeriya. Gwanatin ta bayyana cewa, su dai waɗannan manhajoji da za ta dakatar da su manhajoji ne halastattu da aka yi wa rajista kuma sannan ta saki wani jerin sunayen haramtattun manhajojin ba da rance da suke aiki a ƙasar nan. Hukumar kare masu amfani da kaya/mai saye (FCCPC) ta bayyana haka a ranar alhamis ɗin da ta gabata. Inda suka ƙara da bayyana sunayen manhajojin rancen na yanar gizo waɗanda suka ƙi yin rajista a ƙarƙashin…
Read More
PSG za ta biya Mbappe yuro miliyan 60 a matsayin tukwicin riƙe shi

PSG za ta biya Mbappe yuro miliyan 60 a matsayin tukwicin riƙe shi

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Rahotanni daga birnin Paris na cewa akwai yiwuwar PSG za ta biya ɗan wasanta Kylian Mbappe kuɗaɗen da yawansu ya kai yuro miliyan 60 a matsayin tukwicin yabawa da biyayya ko amintakar da ke tsakaninsu. Bayanan sun ce ƙungiyar ta París Saint Germaine za ta biya tauraron na ta maƙudan kuɗaɗen ne, muddin bai raba gari da ita har zuwa ranar 1 ga watan Agusta, duk da cewar dangantakar da ke tsakaninsu ta yi rauni matuƙa, biyo bayan ƙin tsawaita yarjejeniyarsa da ya yi da ke shirin karewa a 2024. Yanzu haka dai ƙungiyoyi da dama…
Read More
Abdu Maikaba ya zama sabon kocin Kno Pillars

Abdu Maikaba ya zama sabon kocin Kno Pillars

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa ta Kano Pillars ta naɗa Abdullahi Maikaba a matsayin sabon kocinta. Maikaba ya rattaba hannu kan kwangilar shekara biyu da kungiyar da ake kira "Sai Masu gida" daga kakar 2023/2024 zuwa 2024/2025. Kocin zai yi aiki tare da Abubakar Abubakar da ake kira Senior da Ahmad Garba Yaro Yaro da Gambo Muhammad da kuma Auwalu Abbas a matsayin mai horar da masu tsaron gida. Da yake ƙaddamar da kocin a ofishinsa, mataimakin gwamnan jihar Kano, Kwamared Aminu AbdulSalam Gwarzo, ya buƙace shi da ya zage damtse domin farfado da martabar ƙungiyar. Mataimakin gwamnan,…
Read More
Yaƙi da cutar mantuwa a Nijeriya

Yaƙi da cutar mantuwa a Nijeriya

Wani bincike na masana ya nuna cewa ’yan Nijeriya na cikin waɗanda suka fi fama da ciwon mantuwa a duniya. Ciwon mantuwa da ake kira ‘dementia’ na ɗaya daga cikin cututukan da ke barazana ga lafiyar bil’adama a duniya. Wata ƙungiyar da ta gudanar da binciken mai suna 'Alzheimer’s Disease International' ta ce, sama da mutum miliyan 40 ke fama da cutar a duniya ba tare da sun sani ba. Binciken ya kiyasta cewa kashi 75 cikin 100 na ɗauke da cutar ba tare da sun sani ba, kuma waɗannan alqaluma sun fi yawa a ƙasashen Nijeriya da Indiya da…
Read More
Shugabancin APC: NPCF ta yi na’am da naɗin Ganduje

Shugabancin APC: NPCF ta yi na’am da naɗin Ganduje

Daga BASHIR ISAH Kwamitin gudanarwa na ƙasa na ƙungiyar kansilolin jam'iyyar APC (NPCF) ya amince da naɗin tsohon Gwamnan Jihar Kano, Dokta Abdullahi Umar Ganduje, a matsayin sabon Shugaban Jam'iyyar APC na ƙasa. Ƙungiyar ƙarƙashin jagorancin Hon Muslihu Yusuf Ali, ta bayyana haka ne cikin sanarwar manema labarai da ta fitar mai ɗauke da sa hannnun Sakataren Ƙungiyar na Ƙasa, Hon Abayomi A. Kazeem da kwanan wata 29 ga Yuli, 2023. A cewar ƙungiyar, bai wa Ganduje shugabancin jam'iyyar ya yi daidai kasancewar gogaggen ɗan siyasa, ƙwararre wanda ya samar da ɗimbin cigaba a Jihar Kano a zamanin gwamnatinsa. Daga…
Read More
Ɗan El-Rufai ya samu shugabancin kwamitin Majalisa Wakilai

Ɗan El-Rufai ya samu shugabancin kwamitin Majalisa Wakilai

Daga MAHDI M. MUHAMMAD A ranar Alhamis ne aka naɗa Muhammad Bello El-Rufai, ɗan tsohon gwamnan Jihar Kaduna da kuma ɗiyar tsohon gwamnan jihar Delta, James Ibori, Erhiatake Ibori-Suenu, a matsayin shugabannin kwamitoci na dindindin. Kakakin Majalisar Abbas Tajuddeen ne ya sanar da kwamitoci 134 na dindindin a zaman majalisar. Yayin da aka naɗa ɗiyar Ibori a matsayin shugabar kwamitin majalisar wakilai na hukumar raya yankin Neja Delta (NDDC), an bayyana ɗan El-Rufai a matsayin shugaban majalisar dokokin banki. Tsohon mataimakin kakakin majalisar, Ahmed Idris Wase, tsohon shugaban majalisar, Alhassan Ado Doguwa, Yusuf Adamu Gagdi, Mukhtar Betara suma sun zama…
Read More
DSS ta kama tsohon ministan Buhari, Hadi Sirika kan gidogar ‘Nigeria Air’

DSS ta kama tsohon ministan Buhari, Hadi Sirika kan gidogar ‘Nigeria Air’

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ta kama tsohon ministan sufurin jiragen sama a gwamnatin Muhammadu Buhari, Hadi Sirika wanda ya yi amfani da jirgin saman Ethiopia wajen zamba a Nijeriya kimanin Naira biliyan 139.3. Rahotanni sun bayyana cewa, Sirika ya isa hedikwatar DSS da ke Abuja domin amsa tambayoyi a wata mota ƙirar Range Rover SUV a ranar Alhamis, 27 ga watan Yuli, 2023. Rahotanni sun ce jami’an DSS sun yi tsare sa na tsawon sa’o’i. Wannan tuhumar na zuwa ne bayan da muƙaddashin Manajan Daraktan Kamfanin na Nijeriya Air, Captain Dapo Olumide,…
Read More