10
Jun
Daga UMAR M. GOMBE Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa 'yan Nijeriya miliyan ɗaya da matsalar cutar korona ta shafa za su riƙa karɓar N5,000 a kowane wata har tsawon watanni shida. Ta ce wannan ya na cikin wani sabon shiri ne da ya fara aiki a farkon wannan shekarar da mutum 3,115 a Legas da Abuja, wanda yanzu za a faɗaɗa shi zuwa sauran dukkan jihohi inda mutane za su fara amfana da shi su ma. Ministar Harkokin Jinƙai, Agaji da Inganta Rayuwa, Hajiya Sadiya Umar Farouq, ita ta bayyana haka a lokacin wani taron manema labarai da aka yi…
