12
Apr
Daga FATUHU MUSTAPHA Kwamandan rundunar Operation Lafiya Dole, Major-General Faruk Yahaya, ya yi kira ga kafafen yaɗa labarai da su mara wa jami'an tsaro baya domin kawo ƙarshen Boko Haram a Nijeriya. Kwamandan ya yi wannan kira ne yayin wani taron karramawa da aka shirya wa 'yan jarida a Barno a barikin sojoji da ke Maimalari a jihar. General Yahaya ya nuna yabo tare da jinjina ga 'yan jarida inda ya bayyana su a matsayin masu taka muhimmiyar rawa a fagen yaƙi da ta'addanci da ake ci gaba da fafatawa. Ya ci gaba da cewa kafafen yaɗa labarai na da…
