Editor

9513 Posts

Buhari ya jajanta wa Sarauniya Elizabeth kan rasuwar mijinta

Buhari Daga UMAR M. GOMBE Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya miƙa ta'aziyyarsa ga Sarauniya Elizabeth II ta Ingila dangane da rasuwar mijinta Yarima Philip wanda ya bar duniya yana da shekara 99. Buhari ya ce, "rasuwar marigayin alama ce ta ƙarshen wani ƙarni. Yarima Philip ya kasance mutum mai muhimmanci wanda duniya ma ta san da shi, wanda ba za a mance da gudunmawarsa ga ƙasashe renon Ingila ba na tsawon zamunna. "Yarima Philip ya kasance jarumi ne wanda ya yi amfani da dukiyarsa wajen tallafa wa al'umma musamman ma abin da ya shafi tsare gandun daji da sha'anin matasa…
Read More
Biafara na barazana ga Wazobia

Biafara na barazana ga Wazobia

Daga NASIRU ADAMU EL-HIKAYA Kawo ƙarshen yaƙin basasar Nijeriya a 1970 bai zama ƙarshen muradin masu son raba Nijeriya don neman kafa ƙasar Biafara ta ƙabilar Igbo a Kudu maso gabashin Nijeriya ba. Wannan ya nuna dakarun Nijeriya sun ci nasarar wargaza ɗamarar yaƙin ’yan Biafara ne amma waɗannan masu son kafa ƙasar ’yan aware na nan da muradin su. Da alamu su kan ma gadar da muradin ga ’ya'yan su ko da bayan sun mutu masu tasowa su ɗora daga inda suka tsaya har sai sun cimma muradin nasu. Ɓullowar ƙungiyar IPOB ta Nnamdi Kanu ta zama sabuwar tafiya…
Read More
Ilimin ‘ya’ya mata a zamanin da ke wanzuwa

Ilimin ‘ya’ya mata a zamanin da ke wanzuwa

Daga AMINA HASSAN ABDULSALAM A tarihin duniya mata na da wani irin tasiri da muhimanci a rayuwa kasancewarsu iyaye mata ko matan aure, ko ‘ya’ya mata ko kuma dai a taƙaice iyayen al’umma. Gudunmawar mata a cikin al’umma na da dumbin yawan gaske saboda waxan can dalilan da na ambata a sama. Ta hanyar auratayya da su ake haɗa nasaba mai kyau ake kuma faɗaɗa nasabar nan zuwa inda ma ba zata ba. Gudunmawar mata ga cigaban al’umma yana da faɗin gaske kama tun daga lokacin Annabawa zuwa yanzu. A dalilin haka ne ya kyautu a baiwa mace duk wani…
Read More

Shaikh Zakzaky a shekaru 70 masu albarka

Shaikh Zakzaky Daga NAJEEB MAIGATARI A shekarar 2009 an gayyaci Chimamanda Ngozi Ndichie zuwa wani taro da ‘TED talk’ ta shirya a jami’ar Oxford da ke birnin Ingila. Cikin muƙalar da ta gabatar a taron mai taken “The Danger Of A Single Story” ta bayyana hadarin da ke tattare da labari daya tilo mai bangare daya (single story). Cikin jawabin ta a lokacin, Chimamanda ta bayyana irin tasirin da ‘single story’ ya ke da shi ga al’umma, ta yanda cikin ƙanƙanin lokaci ake yarda da wannan labarin, ko da ya saba da abun da ya ke a zahiri. Misali, saboda…
Read More

Tallafin Sadiya Farouq a kan Korona

Sadiya Daga IBRAHIM SHEME A bara ne aka samu ɓullar cutar nan mai suna 'Coronavirus' (COVID-19 a taƙaice), wadda da Hausa ake kira Korona. Cuta ce wadda ta mamaye duniya, ta zama annobar da mu dai a zamanin mu ba mu taɓa ganin irin ta ba. Ta tsiro ne daga birnin Wuhan da ke yankin Hubei na ƙasar Chaina inda daga can ta yaɗu a faɗin duniya. Ta tilasta rurrufe wurare tare da jawo bala'o'i da su ka haɗa da yawan mace-mace, rashin samun kuɗin shiga, hana tafiye-tafiye, rufe masana'antu da wuraren kasuwanci, rasa aikin yi, da kuma tsananin fargaba.…
Read More

Mun yaba da azamar sojojin Nijeriya a baya-bayan nan – Zulum

Gwamna Zulum Daga MUHAMMAD AL-AMEEN, MaiduguriGwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya yaba da ƙoƙarin sojojin Nijeriya dangane da suke yin azama a baya-bayan nan, inda suka fatattaki mayaƙan Boko Haram a ƙoƙarinsu na shiga garin Gwoza da yunƙurin datse hanyar arewacin jihar. Gwamnan ya bayyana haka a wata sanarwar manema labarai mai ɗauke da sa hannun mai taimaka masa kan harkokin yaɗa labarai da hulɗa da jama'a, Malam Isa Gusau, a farkon wannan makon tare da bayyana ƙoƙarin da sojojin suka yi na fatattakar mayaƙan daga garin babban abin yabo ne. “Gwamnan ya jinjina wa sojojin Nijeriya, musamman sojojin…
Read More

Tinubu da ƙurar 2023 a Arewa

Tinubu Daga FATUHU MUSTAPHA ’Yan makonni da suka wuce ne, Gidan Arewa, wato Arewa House, da yake a Kaduna ya bayar da sanarwar tsohon gwamnan Jihar Legas kuma jigo a jam'iyyar APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, zai zama babban baƙo mai jawabi a taron da take shiryawa na shekara-shekara, don tunawa da Sir Ahmadu Bello, Sardaunan Sakkwato, na wannan shekara. Tun bayan da wannan sanarwa ta fito, aka fara cece-kuce a Arewacin ƙasar akan wannan zaɓi na tsohon sanatan. Jim kaɗan bayan taron kuma sai ga wata sanarwar daga hukumomi na cewa, za a yi bikin taya jagoran na APC murnar zagoyawar ranar…
Read More

Bazoum ya naɗa sabbin ministocin sa a Nijar

Shugaba Bazoum Daga UMAR M. GOMBE Sabon Shugaban Ƙasar Jamhuriyar Nijar, Mohamed Bazoum ya naɗa sabbin ministoci da za su yi aiki a gwamnatin sa, kamar yadda sanarwar da Sakataren Gwamnatin ƙasar ta bayyana a ranar Larabar da ta gabata. Sanarwar ta ƙara da cewa, an naɗa sabbin ministoci 33, kuma shida daga cikin su mata ne. Hakan na nufin adadin ministocin ya ragu idan aka kwatanta da ministoci 43 da suka yi aiki a gwamnatin tsohon shugaba Mahaman Issoufou. Naɗin ministocin ya faru ne a yayin da sabon Fira Ministan Jamhuriyar ta Nijar Ouhoumoudou Mahamadu ya sha rantsuwar kama…
Read More

Shugaba Ouattara ya ce Gbagbo da Ble za su iya dawo wa gida

Alassane Ouattara Daga UMAR M. GOMBE Shugaban Ƙasar Kwaddebuwa, Alassane Ouattara ya ce tsohon shugaban ƙasar Laurent Gbagbo da kuma jagoran matasa ’yan gani-kashe-ni da ke mara masa baya wato Charles Ble na iya komawa gida a duk lokacin da suke buƙata, bayan da kotun duniya ta ICC ta wanke su daga laifukan da ake zargin su da aikatawa. Shugaba Ouattara, wanda ke jagorantar taron majalisar ministocin ƙasar a ranar Larabar da ta gabata, ya ce bayan dawowar sa a gida tsohon shugaba Laurent Gbagbo zai ci moriyar illahirin haƙƙoƙin da doka ta ce a bai wa tsohon shugaban ƙasar.…
Read More

Muryar Jama’ar Jigawa ta buƙaci a taimaka wa ‘yan sintiri

Gwamna Badaru Daga UMAR AKILU MAJERI a Dutse Muryar Jama’ar Jihar Jigawa, wato Jigawa Forum tare da haɗin gwiwar masu ruwa da tsaki a jihar sun yi wani gagarimin taro da nufin taimaka wa ƙungiyar 'yan sintiri ta jahar. An gudanar da taron ne a ɗakin taro na otel ɗin Three Star da ke fadar Gwamnatin Jihar ta Jigawa, Dutse, a makon jiya. Ƙungiyar Muryar Jama'ar Jigawa wato Jigawa Forum ta bakin shugaban ta Farfesa Muhammed Tabi'u ta buƙaci gwamnatin jihar ta Jigawa da ta agaza wa ƙungiyar sintirin da kayan aiki da suka haɗa da kayan sarki wato kaki da…
Read More