15
Apr
Daga WAKILINMU Tsohon Shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya, Dakta Abubakar Bukola Saraki ya taya daukacin al’ummar Nijeriya da fadin duniya murnar fara azumin watan Ramadana. Ya kuma yi kira ga ‘yan Nijeriya da su yi amfani da wannan dama wurin yin addu’ar Allah Ya dawo da zaman lafiya, hadin kai da bunkasar Nijeriya. Dakta Saraki ya bayyana haka ne a wata takardar manema labarai wacce Shugaban Sashen yada labarai naa ofishinsa, Yusuph Olaniyonu ya fitar a jiya. Ya ce, watan Ramadan lokaci ne da musulmi za su nemi kusanci ga mahaliccinsu kuma su kyautata alaka a tsakaninsu, musamman yin amfani da…
