Editor

9513 Posts
Marubuci tamkar wata mikiya ce a cikin al’umma – Lantana Ja’afar

Marubuci tamkar wata mikiya ce a cikin al’umma – Lantana Ja’afar

*Ni ce mace ta farko da ta fara lashe gasar 'Gusau Institute'- Lantana Daga AISHA ASAS A wannan makon jaridar Manhaja ta tattauna da Lantana Ja'afar, mace ta farko da ta taɓa cin gasar rubutun labarai ta cibiyar 'Gusau Institute' da suke shiryawa duk shekara. A wannan hirar masu karatu za su ji yadda Lantana ta fara rubutu da kuma ƙalubalen da ta fuskanta a harkar rubutun tare da wasu batutuwa da idan ku ka biyo mu za ku ji su: Mu fara da jin tarihin ki.Assalamu alaikum. Suna na Lantana Ja'afar, an haife ni a shekarar 1988 a cikin…
Read More

Rundunar Ebube Agu ma ta fara cara!

Tawagar Gwamnonin Kudu-maso-gabas Daga NASIRU ADAMU EL-HIKAYA Sabuwar rundunar ’yan banga da gwamnonin Kudu maso Gabashin Nijeriya suka kafa mai taken “Ebube Agu” da harshen Igbo ta fara cara, saboda jagororin kafa ta na da babban muradin farko na hana kiwo a fili, kamar yadda Gwamnan Jihar Binuwai, Samuel Otom, ya zartar, duk da cewa shi ɗan mabilar Tibi ne kuma daga Arewacin Nijeriya. A lokacin da na ga labarin gagarumin tsaron gwamnonin na Igbo a garin Owerri, sai na tuno da kafa irin wannan runduna da tun farko gwamnonin yankin Yarabawa suka yi mai taken “Amotekun” da muradin hana kiwon…
Read More
Kama muggan makamai a Nijer don safarar su zuwa Maiduguri

Kama muggan makamai a Nijer don safarar su zuwa Maiduguri

A kwanan nan ne jami’an tsaro na Jamhuriyar Nijer suka damƙe wasu muggan makamai da ake yunƙurin shiga da su Nijeriya, don kai su Maiduguri, babban birnin jihar Borno, inda aka fi fama da balahirar yaƙin Boko Haram. Jami’an qasar Nijer ɗin ne suka bayyana hakan, inda suka ce sun kama wata mota ƙirar Toyota Hilux danlare da muggana makaman da suka haɗa da harsashi da bindigogi ƙirar AK-47, inda aka cafke su a Agadez bayan sun tsallako daga kan iyakar Ƙasar Libya da nufin tunkrar Nijeriya, domin kai su. Sashen tsaro na Birnin Agadez da ke Nijer shine ya…
Read More
Yaushe Musulunci ya zo ƙasar Hausa?

Yaushe Musulunci ya zo ƙasar Hausa?

Daga INJINIYA AHMED MUHAMMED DAURA Fahimtar takamaiman lokacin da Musulunci ya fara zuwa ƙasar Hausa abu ne mawuyaci, saboda da farko dai babu wani tarihin da ya bayyana wata ƙungiya ko ƙabilar da ta kawo jihadi ko wani yaƙin musuluntar da Hausawa. Bisa ga wannan dalilin za a karɓi Musulunci ya fara zuwa ƙasar Hausa daga ɗaiɗaikun mutane, watau baƙin Musulmai. A nazarin baƙin Musulmai ya bada damar fahimtar abokan hulɗar ƙasar Hausa, wanda ya ƙunshi mashahuriyar cinikayyar Hausa da tsallaken hamada (Trans-Saharan Trade) kamar sassan Aljeriya da Libya na yanzu zuwa Rum da Turai, tsallaken tekun maditareniya. Hanyoyin sun…
Read More
Za a buɗe hanyar saida sabbin layukan sadarwa 19 ga Afrilu, cewar Gwamnati

Za a buɗe hanyar saida sabbin layukan sadarwa 19 ga Afrilu, cewar Gwamnati

Daga AISHA ASAS Gwamnatin Tarayya ta bada sanarwar cewa ya zuwa ranar 19 ga Afrilun da muke ciki za a buɗe hanya don bada famar mallakar sabon layin sadarwa (SIM CADR) ga masu buƙata. Gwamnatin ta ce hakan zai tabbata ne bayan kammala tantancewa da kuma tabbatar da kiyaye dokoki yadda ya kamata. Ma'aikatar Sadarwa da Tattalin Arzikin Intanet ita ce ta yi wannan bayani a wata sanarwar manema labarai da ta sami sa hannun hadimini ministan sadarwa, Femi Ademiluyi. Idan dai za a iya tunawa a Disamban 2020 ne gwamnati ta dakatar da saida layukan sadarwa da nufin tantance…
Read More
Nijar: Yadda gobara ta ci ƙananan yara 20 a makaranta

Nijar: Yadda gobara ta ci ƙananan yara 20 a makaranta

Daga BASHIR ISAH Ƙananan yara 'yan makaranta kimanin su 20 aka ruwaito sun halaka a ƙasar Nijar sakamakon gobarar da ta auku a wata makaranta. Wannan mummunan al'amari ya faru ne a Talatar da ta gabata a gefen Niamey, babban birnin ƙasar, inda iyaye da malamai haɗa da sauran al'ummar yankin suka kasance cikin alhini mara misaltuwa. Gobarar ta ci yaran ne a cikin azuzuwan da aka gina da katakai, kamar yadda shaidu suka bayyana. Daraktar makarantar, Habiba Gaya, cikin kuka da hawaye ta faɗa wa jaridar AFP cewa haka yaran suka ƙone a cikin gobarar. Ta ce wasu daga…
Read More
Gwamnatin Tarayya ta bai wa ‘Yan Nijeriya haƙuri kan ƙarancin wutar lantarki

Gwamnatin Tarayya ta bai wa ‘Yan Nijeriya haƙuri kan ƙarancin wutar lantarki

Daga FATUHU MUSTAPHA Gwamnatin Tarayya ta bai wa 'yan Nijeriya haƙuri dangane da matsalar ƙarancin wutar lantarki da ake fama da ita a sassan ƙasa. Hakan ya faru ne sakamakon akasin da aka samu a wasu cibiyoyin da ke samar wa ƙasa da lantarki, in ji Ma'aikatar Lantarki ta Ƙasa. Mai bai wa Ministan Lantarki Shawara Kan Harkokin Yaɗa Labarai da Sadarwa, Aaron Artimas, ya lissafo cibiyoyin da matsalar ta shafa da suka haɗa da cibiyar lantarki ta Sapele, ta Afam, ta Olonrunsogo, ta Omotosho, ta Ibom, ta Egbin, ta Alaoji, da kuma ta Ihovbor. Ya ƙara da cewa an…
Read More
Cross River: Shirin sauya sheƙar Gwamna Ayade ya kaɗa hanjin PDP

Cross River: Shirin sauya sheƙar Gwamna Ayade ya kaɗa hanjin PDP

Daga UMAR M. GOMBE Domin gudun kada ta rasa ɗanta, Jam'iyyar PDP ta tura a rarrashi Gwamnan Jihar Cross River, Ben Ayade,bayan da ta gano cewa gwamnan na shirin sauya sheƙa zuwa APC. Binciken Manhaja ya gano cewa matakin sauya sheƙar da Gwamna Ayade ya ɗauka ba ya rasa nasaba da rasa ƙarfin ikon jan akalar PDP a jihar ga 'yan majalisar ƙasa daga jihar kamar yadda ya bayyana yayin wani taro da suka gudanar kwannan nan. Haka nan, Manhaja ta tattaro cewa ɗaukacin shugabannin ƙananan hukumomin jihar su 18 da kansilo196 ba su saɓa wa umarnin gwamnan saboda cikakkiyar…
Read More
An dangata wasu tsoffin gwamnonin Nijeriya da dukiyar sata a Birtaniya

An dangata wasu tsoffin gwamnonin Nijeriya da dukiyar sata a Birtaniya

Daga WAKILINMU Wani sabon rahoto da aka fitar kwannan ya nuna yadda wasu tsofoffin gwamnonin Nijeriya su goma ke da alaƙa da wasu tarin haramtattun kadarori a Ƙasar Birtaniya wanda darajarsu ta kai Pan milyan £56, wato kwatankwacin Naira bilyan N30 kenan. Rahoton kan hada-hadar haramtattun kuɗaɗe (IFF) daga Nijeriya zuwa Birtaniya da Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa (UAE) ya kuma nuna wasu kadarori 216 mallakar wasu jami’an Nijeriya su 13 da aka girke Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa. A cewar jaridar SaharaReporters, an gabatar da rahoton ne a wajen taron da cibiyar Human and Environmental Development Agenda tare da haɗin gwiwar Gidauniyar MacArthur…
Read More
Gwamnati na aiki tuƙuru kan karɓo sauran ‘yan matan Chibok – Minista Sadiya

Gwamnati na aiki tuƙuru kan karɓo sauran ‘yan matan Chibok – Minista Sadiya

Daga AISHA ASAS Ministar Harkokin Jinƙai, Agaji da Inganta Rayuwa, Hajiya Sadiya Umar Farouq, ta bayyana cewa Gwamnatin Tarayya ta na ci gaba da aiki ba tare da gajiyawa ba domin ta ceto sauran 'yan matan Chibok waɗanda aka sace shekaru bakwai da su ka gabata. Ministar ta yi wannan maganar ne a ranar Laraba lokacin da ta ke jimamin abin baƙin cikin nan da ya faru na satar ɗaruruwan 'yan matan daga makarantar su ta kwana da ke garin Chibok a Jihar Borno. Mayaƙan Boko Haram ne su ka sace 'yan matan. Sadiya Farouq ta ce ta na matuƙar…
Read More