18
Apr
Daga BASHIR ISAH Bayanai daga jihar Ekiti sun tabbatar da mutuwar wasu mutum shida sakamakon rikicin da ya ɓarke a tsakanin ƙungiyoyin asiri a yankin Ikere na jihar. Mai magana da yawun 'yan sandan jihar, Sunday Abutu, ya tabbatar wa manema labarai da faruwar haka. Jami'in ya ce sun gano gawarwakin mutum shida da aka kashe sakamakon rikicin wanda ya auku da sanyin safiyar Lahadi. Wata majiya daga yankin da abin ya faru ta ce an ji ƙarar harbe-harben bindigogi yayin rikicin lamarin da ya tilasta wa mazauna yankin gudun neman mafaka don tsira da rayuwarsu. Abutu ya ce waɗanda…
