Editor

9513 Posts
Shugaban Chadi, Idris Deby ya rasu

Shugaban Chadi, Idris Deby ya rasu

Daga UMAR M. GOMBE Rahotanni daga ƙasar Chadi sun tabbatar da rasuwar Shugaban Ƙasar, Idris Deby Itno, mai shekaru 68. Bayanan sojojin ƙasar sun nuna marigayin ya kwanta dama ne sakamakon raunukan da ya samu a karawar da ya jagoranci dakarunsu wajen fatattakar ‘yan tawayen FACT na ƙasar. Bayanan sosjojin sun sake nuna cewa, marigayi Deby ya rasu ne jim kaɗan bayan sanar da nasarar da ya samu a babban zaɓen ƙasar da aka gudanar a ranar 11, Afrilu, 2021. A cewar Hukumar Zaɓen Chadi, marigayin ya lashe zaɓen ne da kashi 79.32 na yawan ƙuri’un da aka kaɗa. Sanarwa…
Read More
Hukumar Zaɓe za ta hukunta jam’iyyu masu yin rikici a babban taron su

Hukumar Zaɓe za ta hukunta jam’iyyu masu yin rikici a babban taron su

Daga WAKILINMU Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta yi barazanar za ta hukunta duk wata jam'iyyar siyasa wadda ta kasa gudanar da babban taron ta (congress) cikin lumana. A cikin wata sanarwa da ta bayar a ranar Litinin, INEC ta ce akwai yiwuwar ba za ta amince da sakamakon da aka samar a babban taron jam'iyyar da aka yi a cikin hatsaniya ba idan har ba a daina wannan ɗabi'ar ba. Kakakin hukumar, Mista Festus Okoye, ya ce ƙazancewar rikicin da ake samu a wajen babban taron jam'iyya ya na sanyawa hukumar ta samu “matuƙar wahala” wajen gudanar da aikin…
Read More
Maniyyatan Pakistan 50,000 ne za su sauke farali bana

Maniyyatan Pakistan 50,000 ne za su sauke farali bana

Daga AISHA ASAS Kimanin maniyyata 40,000 zuwa 50,000 daga ƙasar Pakistan ake sa ran za su yi aikin Hajjin bana, in ji Ministan Harkokin Addini na Ƙasar, Sahibzada Noor-ur-Haq Qadri. Ministan ya bayyana haka ne a Lahadin da ta gabata, tare da cewa hajjin bana zai gudana ne ƙarƙashin kulawa ta musamman saɓanin yadda aka saba gani a baya, inda aka gindaya dokoki da sharuɗɗa na musamman. Ya ce ana buƙatar maniyyatan su bi ƙa'idojin da aka shimfiɗa sau da ƙafa yayin aikin hajjin. Ya ci gaba da cewa, maniyyatan da aka tabbatar sun yi allurar rigakafin korona kaɗai za…
Read More
Mutum biyu sun rasu a haɗarin hanyar Kaduna

Mutum biyu sun rasu a haɗarin hanyar Kaduna

An yi fargabar wasu mutum biyu sun mutu sakamakon wani mummunan haɗarin da ya faru a yankin Jere kan babbar hanyar Kaduna zuwa Abuja a wannam Litinin. Bayanan da Manhaja ta tattara sun nuna motoci biyun da haɗarin ya rutsa da su sun baro Abuja zuwa Kano ne inda akasin ya auku. Ya zuwa haɗa wannan labari, ba a bayyana dalilin aukuwar haɗarin ba. Tuni dai labarin aukuwar haɗarin ya isa ofishin jami'an kiyaye haɗurran kan haya mafi kusa.
Read More
‘Yan sandan Nijeriya 144 sun isa ƙasar Somaliya domin aikin bada tsaro

‘Yan sandan Nijeriya 144 sun isa ƙasar Somaliya domin aikin bada tsaro

Daga WAKILINMU Nijeriya ta tura gudunmawar 'yan sanda su 144 ya zuwa ƙasar Somaliya domin aikin tallafa wa fannin tsaron ƙasar. Nijeriya ta tura jami'an nata ne ƙarƙashin tawagar AMISOM ta ƙungiyar tarayyar Afirka (AU). Babban jami’in tsare-tsare na tawagar AMISOM a ƙasar, Daniel Ali Gwambal, ya bayyana cewa 30 daga cikin 'yan sandan za su yi aiki na tsawon shekara guda ƙarƙashin tawagar AMISOM, inda za a tura su yankunan Beletweyne da ke jihar HirShabelle, sauran kuma za su yi aiki a sassan birnin Mogadishu babban birnin ƙasar. Jami'in ya ce sauran ‘yan sandan za su yi ayyukan tsaro…
Read More
Zanga-zanga: An hana lauyoyi shiga Majalisar Tarayya

Zanga-zanga: An hana lauyoyi shiga Majalisar Tarayya

Daga AISHA ASAS Jami'an tsaro a Abuja, sun hana tawagar lauyoyi da suka yi zanga-zanga shiga Majalisar Tarayya. A wannan Litinin mambobin Ƙungiyar Lauyoyi ta Ƙasa (NBA) suka gudanar da zanga-zangar lumana zuwa Majalisar inda suka tarar da jami'an tsaro girke a ƙofar shiga majalisar. Manhaja ta gano cewa lauyoyin sun yin zanga-zangar ne domin nuna goyon baya da haɗin kai ga ma'aikatan fannin shari'a dangane da 'yancin gashin kan da suke nema na sarrafa kuɗaden gudanarwa. Tun farko sai da lauyoyin suka yi dafifi a ƙofar shiga Kotun Ɗaukaka Ƙara kafin daga bisani suka ɗunguma zuwa Majalisar Tarayya inda…
Read More
‘Yan bindiga sun yi kaca-kaca da ofishin ‘yan sanda a Imo

‘Yan bindiga sun yi kaca-kaca da ofishin ‘yan sanda a Imo

Bayanan da Manjaha ta samu ba da jimawa ba daga jihar Imo, sun nuna wasu 'yan bindiga da ba a kai ga sanin ko su wane ne ba a jihar, sun kai wa sabon hedikwatar 'yan sanda na 'Zone 13' da ke Ukpo hari inda suka banka wa ofishin wuta suka yi kaca-kaca da shi. Binciken Manhaja ya gano cewa 'yan sanda biyu sun rasu sakamakon harin, yayin da motoci da dama sun ƙone. Ƙazamin harin wanda aka kai a wannan Litinin, ya zuwa haɗa wannan labari hukumomi ba su ce komai a kai ba. Ko a 'yan makonnin da…
Read More
Za a soma gwanjon duk shanun da aka kama da lalata gona a Ondo

Za a soma gwanjon duk shanun da aka kama da lalata gona a Ondo

Daga WAKILINMU Gwamnatin jihar Ondo ta ce daga yanzu za ta riƙa gwanjon duk shanun da ta kama da laifin ɓarna a gona tare da hukunta masu shanun a bisa umarnin kotu. Shugaban 'yan bangan Amotekun na jihar, Cif Adetunji Adeleye, shi ne ya bayyana hakan a lokacin da yake rattaba hannu kan yarjejeniyar sakin shanu sama da 250 da Amotekun suka kama a Akure, babban birnin jihar. A cewar Adeleye Amotekun ta kama shanu sama da 250 a cikin jihar biyo bayan ƙorafe-ƙorafen da manoman yankin Ipogun da Ilara da Owena Dam a ƙaramar hukumar Ifedore ta jihar suka…
Read More
Zaɓen 2023 da kamar wuya muddin ba a magance matsalar tsaro ba – Ejiofor

Zaɓen 2023 da kamar wuya muddin ba a magance matsalar tsaro ba – Ejiofor

Daga UMAR M. GOMBE Tsohon Daraktan Sashen Tsaron DSS, Mike Ejiofor, ya ce duba da yadda fannin tsaron ƙasar nan ke ta sukurkucewa ya sa yake ganin da kamar wuya a iya gudanar da zaɓuɓɓukan 2023. Ejiofor ya yi wannan bayani ne yayin hirar da aka yi da shi a tashar Channels a ranar Litinin. Ya ce tun dare bai yi mata ba ya kamata Gwamnatin Tarayya ta gaggauta ɗaukar matakin daƙile wannan matsalar da ta yi wa ƙasa tarnaƙi. Yana mai cewa, “Muddin ba a magnace matsalar tsaron da ta addabi sassan ƙasa kafin zaɓuɓɓukan 2023 ba, ina mai…
Read More