Editor

9513 Posts
Ƙoƙarin da Nijeriya ke yi don kauce wa sake fama da annobar korona, Ministan Lafiya

Ƙoƙarin da Nijeriya ke yi don kauce wa sake fama da annobar korona, Ministan Lafiya

Daga UMAR M. GOMBE Gwamnatin Tarayya ta bada haske kan wasu matakan da ta ɗauka domin tabbatar da Nijeriya ba ta yi fama da ɓarkewar annobar korona karo na uku ba. Yayin da wasu ƙasashen duniya suka soma sake fama da bugun annobar karo karo na uku, Ministan Lafiya, Dr Osagie Ehanire ya ce Nijeriya za ta ci gaba da aikin gwaje-gwaje da take yi domin ganowa, killacewa da kuma kula da waɗanda suka kamu da cutar. Ehanire ya bayyana haka ne a Litinin da ta gabata a Abuja yayin da kwamitin Shugaban Ƙasa kan Yaƙi da Cutar Korona ke…
Read More
Kwastam ta kama shinkafar ƙetare buhu 905 a cikin makonni biyu

Kwastam ta kama shinkafar ƙetare buhu 905 a cikin makonni biyu

Daga AISHA ASAS Hukumar Yaƙi da Fasa-ƙwauri ta Nijeriya ta 'Zone B' a Kaduna, ta baje kolin tarin kayayyakin da ta kama an yi fasa-ƙwaurinsu a tsakanin makonni biyu, a Maris. A cewar Comptroller Al-Bashir Hamisu, sun samu nasarar kama waɗannan kayayyaki ne a wurare daban-daban a shiyyar. Daga cikin kayayyakin da hukumar ta ce ta kama har da shinkafar ƙetare buhu 905 da man girki jarka 541 da dila 138 na gwanjon sutura da motoci guda 6 da dai sauransu. Ga baki ɗaya, hukumar ta ce harajin da ya kamata a biya a kan waɗannan kayayyaki ya kai naira…
Read More
Hajjin 2021: Sarki Aminu ya gargaɗi maniyyatan Kano

Hajjin 2021: Sarki Aminu ya gargaɗi maniyyatan Kano

Daga UMAR. M. GOMBE Mai Marta Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero, ya gargaɗi maniyyatan jihar Kano na Hajjin 2021 kan su kiyaye ban da karya dokoki ciki har da dokokin yaƙi da cutar korona da na tafiya ƙasa da ƙasa yayin da suka isa ƙasa mai tsarki, Saudiyya. Basaraken ya ƙarfafa kan buƙatar maniyyatn su zamo masu biyayya ga dokin yaƙi da korona kana su rungumi ɗabi'ar tsafta yayin da suka shiga aikin Hajji a Daular Saudiyya. Sarkin ya yi wannan gargaɗi ne yayin da yake buɗe taron bita kan aikin Hajji na 2021 a Kano. Taron wayar da…
Read More
Buhari ya karɓi baƙuncin Bankole da Gbenga Daniel

Buhari ya karɓi baƙuncin Bankole da Gbenga Daniel

Daga FATUHU MUSTAPHA Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya karɓi bakuncin tsohon Shugaban Majalisar Wakilai, Mr Dimeji Bankole da tsohonn Gwamnan Jihar Ogun, Mr Gbenga Daniel a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja bayan da suka sauya sheƙa zuwa jam'iyyar APC. Tawagar ta ziyarci Fadar Shugaban ƙasar ne ƙarƙashin jagoranci Shugaban Kwamitin Riƙo na APC kuma gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni tare da Gwamna Abubakar Atiku Bagudu na jihar Kebbi da kuma Gwamna Mohammed Badaru na Jigawa. Da yake amsa tambayoyin manema labarai jim kaɗan bayan kammala ganawarsu, Mai Mala Buni ya ce Shugaba Buhari ya yi matuƙar farin ciki…
Read More
Matawalle ya sha rantsuwa kan ba shi da hannu a matsalar tsaron Zamfara

Matawalle ya sha rantsuwa kan ba shi da hannu a matsalar tsaron Zamfara

Daga WAKILINMU Gwamnan jihar Zamfara, Bello Matawalle, ya yi rantsuwa da Ƙur'ani kan cewa ba shi da wata alaka da 'yan bindigar da ke addabar jiharsa. Gwamnan ya ƙalubalanci mazauna jihar, da su ma su kwatanta shan ranstuwa kamar yadda ya yi domin tabbatar da cewa ba su da hannu cikin matsalar tsaro da ta addabi jihar. Gwamnan ya yi hakan ne a ranar Lahadi a garin Gusau, babban birnin jihar yayin karɓar lambar yabo da Cibiyar Karatun Ƙur'ani ta Nijeriya ta ba shi a matsayin Khadimul Ƙur'an. Ya ce kamar yadda ya sha faɗa lamarin rashin tsaron nan ba gwamnatin…
Read More
Buhari, gwamnoni sun yi tir da harin da aka kai wa Gwamna Ortom

Buhari, gwamnoni sun yi tir da harin da aka kai wa Gwamna Ortom

Daga UMAR M. GOMBE Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya yi martani kan harin da 'yan bindiga suka kai wa Gwamna Samuel Ortom na jihar Binuwai. 'Yan bindiga sun bude wa tawagar gwamnan wuta ne a lokacin da yake dawowa daga gonarsa a ranar Asabar da ta gabata. Tun bayan aukuwar lamarin 'yaan ƙasa da dama sun yi ta faɗin albarkacin bakunansu game da harin inda wasunsu suka yi kira ga gwamnatin tarayya da ta magance ƙallubalen tsaro da ke adabar sassan ƙasar nan. cikin sanarwar da ya fitar a daren Lahadi, shugaba Buhari ta bakin kakakinsa Garba Shehu, ya yi tir da…
Read More
Za a soma aikin gyaran gada a Legas

Za a soma aikin gyaran gada a Legas

Daga FATUHU MUSTAPHA Gwamnatin Tarayya ta bada tabbacin cewa nan bada daɗewa ba, za ta soma aikin gyran gadar hanyar zuwa filin jirgin sama a birnin Legas wadda ta ƙone a lokutan baya. Babban Sakataren Ma'aikatar Ayyuka a Gidaje ta Tarayya, Alhaji Babangida Hussaini, shi ne ya faɗi haka yayin wani rangadi da ya yi a Legas domin duba wasu ayyukan gidaje da hanyoyi da ke gudana a jihar. Gadar da lamarin ya shafa ta ci wata ne sakamakon haɗarin tankar mai da ya auku a Janairun da ya gabata, kuma a wancan lokaci aka rufe gadar aka hana abubuwan…
Read More
Tsaro: Shugaban jaridun Manhaja da Blueprint ya buƙaci a kyautata alaƙa tsakanin kafafen yaɗa labarai da gwamnati

Tsaro: Shugaban jaridun Manhaja da Blueprint ya buƙaci a kyautata alaƙa tsakanin kafafen yaɗa labarai da gwamnati

Daga AISHA ASAS Shugaban jaridun Manhaja da Blueprint, Alhaji Mohammed Idris Malagi, ya yi kira da a ƙarfafa haɗin gwiwa da yin aiki tare tsakanin kafafen yaɗa labarai da kuma gwamnati wajen daƙile matsalolin tsaron da suka addabi ƙasa. Alhaji Idris ya yi wannan kira ne a wajen taron makon 'yan jarida wanda Ƙungiyar 'Yan Jarida ta Ƙasa (NUJ) Reshen Jihar Neja ta gudanar ranar Asabar a Minna, babban birnin jihar. A matsayinsa na babban baƙo mai jawabi a wajen bikin, inda ya yi bayani a kan batun: Kafafen Yaɗa Labarai da Matsalar Tsaro a Nijeriya: Lamari da ya Shafi…
Read More
Jam’iyyu 18 kaɗai INEC ta sani a yanzu, inji Okoye

Jam’iyyu 18 kaɗai INEC ta sani a yanzu, inji Okoye

Daga FATUHU MUSTAPHA Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta bayyana cewa ita jam'iyyun siyasa 18 kaɗai ta sani kuma su ne za ta yi aiki da su har sai Kotun Ƙoli ta gama yanke hukunci kan jam'iyyun da aka soke rajistar su. Babban Kwamishina kuma shugaban Kwamitin Wayar da kan Masu Zaɓe da Yaɗa Labarai na hukumar, MistaFestus Okoye, shi ne ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da ya raba wa manema labarai. A sanarwar, ya yi kira ga jam'iyyu 74 waɗanda hukumar ta soke rajistar su da su jira hukuncin na Kotun Ƙoli. Okoye ya ce, “Hukumar Zaɓe…
Read More
Ogun: ‘Yan bindiga sun sace Sarkin Ijebu-Igbo

Ogun: ‘Yan bindiga sun sace Sarkin Ijebu-Igbo

Daga WAKILINMU Rahotanni daga yankin Ijebu-Igbo a jihar Ogun sun nuna wasu 'yan bindiga sun sace sarkin yankin, Oba Alade Meta, a ranar Asabar. Wata majiya ta ce a wannan rana, sarkin ya bar fadarsa da misalin ƙarfe 11 da wata motarsa 'jeep' zuwa unguwa. A kan hanyarsa ta komawa gida misalin ƙarfe 3 na rana, 'yan bindiga suka tare shi a hanya, suka fidda shi a motarsa tare da yin awon gaba da shi sanna suka bar motar tasa a nan. Tun daga wannan lokaci ya zuwa haɗa wannan labari, babu wanda ya san inda sarkin yake. Haka ma…
Read More