12
Feb
Daga BASHIR ISAH An bayyana cewa galibin makiyayan da ke halaka mutane a ƙasar nan ba 'yan asalin Nijeriya ba ne. Bayanin haka ya fito ne ta bakin Gwamna Samuel Ortom na jihar Binuwai yayin wani taron manema labarai da ya gudana a Abuja a ranar Alhamis da ta gabata. Ortom ya yi kira ga Shugaba Muhammadu Buhari da ya buƙaci a sake waiwayar dokokin ECOWAS don yin gyarar fuska dangane da sha'anin zirga-zirgar mutane da kayayyaki a nahiyar Afirka. Ya ce makiyaya daga wajen Nijeriya na amfani da damar zirga-zirga wajen ruruta matsalolin tsaro. Ta bakinsa, "Ƙasashe maƙwabta irin…