Editor

9301 Posts
Galibin makiyayan da ke halaka mana mutane ba ‘yan Nijeriya ba ne, inji Ortom

Galibin makiyayan da ke halaka mana mutane ba ‘yan Nijeriya ba ne, inji Ortom

Daga BASHIR ISAH An bayyana cewa galibin makiyayan da ke halaka mutane a ƙasar nan ba 'yan asalin Nijeriya ba ne. Bayanin haka ya fito ne ta bakin Gwamna Samuel Ortom na jihar Binuwai yayin wani taron manema labarai da ya gudana a Abuja a ranar Alhamis da ta gabata. Ortom ya yi kira ga Shugaba Muhammadu Buhari da ya buƙaci a sake waiwayar dokokin ECOWAS don yin gyarar fuska dangane da sha'anin zirga-zirgar mutane da kayayyaki a nahiyar Afirka. Ya ce makiyaya daga wajen Nijeriya na amfani da damar zirga-zirga wajen ruruta matsalolin tsaro. Ta bakinsa, "Ƙasashe maƙwabta irin…
Read More
Gwamna Bello ya naɗa sabon shugaban ma’aikata

Gwamna Bello ya naɗa sabon shugaban ma’aikata

Daga FATUHU MUSTAPHA Gwamnan jihar Kogi, Alhaji Yahaya Bello, ya naɗa Mrs. Hannah Odiyo a matsayin sabuwar Shugaban Ma'aikata na Gwamnatin Jihar. Sakataren Gwamnatin Jihar, Dr. Folashade Arike Ayoade ne ya sanar da hakan a wata sanarwa da ya fitar a ranar Alhamis. Kafin naɗin nata, Mrs. Odiyouta ta kasance riƙe da matsayin sakatariyar Ma'aikatar Harkokin Noma na Jihar Kogi. Gwamna Bello ya yi yabo na musamman ga shugabar ma'aikata mai barin gado, Deborah Ogunmola dangane da irin gudunmawar da ta bayar ga cigaban sha'anin aikin gwamanti a jihar. Kana ya taya sabuwar shugabar murnar samun sabon muƙami tare da…
Read More
Ɓata-gari sun far wa jami’an Kwastam a Ogun

Ɓata-gari sun far wa jami’an Kwastam a Ogun

Daga AISHA ASAS Hukumar Yaƙi da Fasa-ƙwauri ta Ƙasa a Jihar Ogun, ta ce wasu 'yan fasa-ƙwauri sun kai wa jami'anta hari a bakin aiki a Larabar da ta gabata inda aka yi musayar wuta wanda hakan ya yi sanadiyar mutuwar wani mazaunin ƙauyen Ohunbe mai suna Tunde Alabe. A cewar hukumar an yi arangamar ne a lokacin da jami'an kwastam suka yi ƙoƙarin daƙile fasa-ƙwaurin fetur zuwa ƙetare da masu harkar suka so yi. Ta ce ɓata-garin sun far wa jami'anta ne ɗauke da muggan makamai da suka haɗa da sanduna da bindigogi da dai makamantansu. Lamarin ya yi…
Read More
Buhari ya nuna alhininsa kan rasuwar Jakande

Buhari ya nuna alhininsa kan rasuwar Jakande

Daga FATUHU MUSTAPHA Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya nuna alhininsa dangane da mutuwar tsohon gwamnan jihar Legas, Chief Lateef Jakande, wanda Allah Ya yi wa cikawa a Alhamis da ta gabata. Sanarwar da ta fito ta hannun mai bai wa shugaban shawara kan sha'anin labarai da hulɗa da jama'a, Femi Adesina, Buhari ya ce marigayin ya yi rayuwa irin wadda al'umma ta amfana da ita. Sanarwar ta bayyana Jakande a matsayin mutum wanda ƙasa da al'umma suka amfana da rayuwarsa, wanda za a daɗe ana tunawa da kyawawan ayyukan da ya gudanar. Buhari ya miƙa ta'aziyyarsa ga iyalan marigayin gami…
Read More
Gwamnati ta amince da shirin kula da dattawa, inji Minista Sadiya

Gwamnati ta amince da shirin kula da dattawa, inji Minista Sadiya

Daga WAKILIN MU Majalisar Gudanarwa ta Tarayya (FEC) ta amince da sabon Shirin Kula Da Masu Manyan Shekaru ta Ƙasa, a turance 'National Policy on Aging', a matsayin wani ɓangare na ƙoƙarin da Gwamnatin Tarayya ke yi na tabbatar da tsaron lafiya da tattalin arzikin mutanen da yawan shekaru ya cim masu. Ministar Harkokin Jinƙai, Agaji da Inganta Rayuwa, Hajiya Sadiya Umar Farouk, ita ce ta bayyana haka ga manema labarai a Fadar Shugaban Kasa da ke Abuja a ranar Laraba, jim kaɗan bayan taron hukumar, wanda Shugaba Muhammadu Buhari ya jagoranta. A cewar ta, manufar shirin ita ce domin…
Read More
Fintiri ya ƙaddamar da hanyoyi a Adamawa

Fintiri ya ƙaddamar da hanyoyi a Adamawa

Daga BASHIR ISAH Gwamnan jihar Adamawa Ahmadu Umaru Fintiri ya ƙaddamar da hanyoyi na sama da kilomita 340 a sassan jihar da zimmar sauƙaƙa wa 'yan karkara sha'anin zirga-zirga Aikin samar da hanyoyin haɗin guiwa ne tsakanin gwamnatin Adamawa da Bankin Duniya da cibiyar French Development Agency ƙarkarshin Shirin Samar wa Karkara Hanyoyi na Gwamnatin Tarayya (RAMP-2). Hanyoyin da aka aka ƙaddamar sun shafi ƙananan hukumomi 21 da jihar ke da su ne. Yayin da yake magana a wajen ƙaddamar da hanyoyin, Gwamna Fintiri ya ce gwamnatinsa ba ta sa wasa ba wajen biyan kasonta ga shirin haɗin guiwar wanda…
Read More
Peters ya maye gurbin Farfesa Adamu a NOUN

Peters ya maye gurbin Farfesa Adamu a NOUN

Daga FATUHU MUSTAPHA Farfesa Olufemi A. Peters ya kama aiki a matsayin sabon Mataimakin Shugaban Buɗaɗɗiyar Jami'ar Nijeriya (NOUN) inda ya maye gurbin Farfesa Abdalla Uba Adamu wanda wa'adin aikinsa ya kammala a ranar Laraba, 10 ga Fabrairun 2021. Da yake jawabi yayin bikin karɓar ragamar aiki da ya gudana a ranar Alhamis a Abuja, Petaers ya bayyana cewa jami'ar ba za ta taɓa mancewa da gudunmawar da Adamu ya bayar wajen cigabanta ba a zamaninsa. Ya ce, "Zamanin Farfesa Adamu a jami'ar abu ne da ba za a manta da shi ba, kuma zai zama abin kwatance a gare…
Read More
Runduna ta ƙaryata labarin kashe sosjoji 20

Runduna ta ƙaryata labarin kashe sosjoji 20

Daga FATUHU MUSTAPHA Rundunar Sojojin Nijeriya ta ƙaryata labarin da wata jaridar intanet ta buga mai nuni da 'yan Boko Haram da mayaƙan ISWAP sun kashe sojoji 20 a yankin Arewa maso-gabas. A sanarwar da rundunar ta fitar a Alhamis, Daraktan Sashen Hulɗa da Jama'a na rundunar, Brig.-Gen Mohammad Yerima, ya ce wannan labari ba shi da tushe balle makama. Ya ce an yaɗa labarin ne da manufar sanyaya wa al'umma guiwa game da sha'anin yaƙi da matsalolin tsaro da sojojin ke yi da ma su kansu sojojin da ke yaƙin. A cewarsa harin baya-bayan nan da aka kai wa…
Read More
Tsohon gwamnan Legas ya rasu

Tsohon gwamnan Legas ya rasu

Daga AISHA ASAS Allah ya yi wa gwamnan farar hula na farko a jihar Legas, Lateef Kayode Jakande rasuwa. Marigayin ya bar duniya yana da shekara 91. A halin rayuwarsa, Jakande wanda tohon ɗanjarida ne, ya yi gwamna a Jihar Legas daga 1979 zuwa 1983. Haka nan, ya riƙe muƙamin Ministan Ayyuka a zamanin mulkin marigayi Sani Abacha. An haifi marigayin ne a ranar 23 ga Yulin 1929, a Legas. Gwamnan Legas, Babajide Sanwo-Olu, ya nuna alhinin dangane da rasuwar, tare da bayyana marigayin a matsayin babban rashi.
Read More
Hukumar Kwastam ta kama haramtattun kayayyaki

Hukumar Kwastam ta kama haramtattun kayayyaki

Daga WAKILIN MU Ofishin Hukumar Yaƙi da Fasa-ƙwauri ta Ƙasa na 'Zone C', ya ce ya samu nasarar kama kayayyakin da aka haramta shigo da su cikin ƙasa wanda harajinsu ya haura milyan N869 a Janairun da ya gabata. Kayayyakin da ofishin ya ce ya kama ciki har da katan 1,024 na magungunan da ba a yi musu rajista ba, da shinkafar ƙetare buhu 1,046, da katan 62 na sabulun, da mota ƙirar Toyota da dai sauransu. A cewar Comptroller Yusuf Lawal, haƙƙinsu ne tabbatar da cewa ana kiyaye dukkan ƙa'idojin da gwamnati ta shimfiɗa dangane da haramcin shigo da…
Read More