Editor

9441 Posts
Yadda wasan damben gargajiya ke karɓuwa a Nijeriya

Yadda wasan damben gargajiya ke karɓuwa a Nijeriya

Daga FATUHU MUSTAPHA Wasan damben gargajiya baya buƙatar wani dogon gabatarwa ga masu karatu, domin wasa ne da ya shahara ba ma a nan ƙasar ba, har ma faɗin Afrika ta Yamma gaba ɗaya. Hausawa dai kan masa kirari da “Saga wasan mahaukata, mai hankali yana na daina mahaukaci yana zan fara.” Ba muda wani cikakken bayani akan lokacin da aka fara wasan damben a tarihin Ƙasar Hausa, sai dai shaidu na tarihi sun nuna irin tasirin sa a rayuwar Bahaushe tun shekaru aru aru da suka shuɗe. Babban misali na daɗewar wasan dambe shi ne abinda muka samu daga…
Read More
Wanzar da zaman lafiya haƙƙi ne a kanku, cewar Hukumar Abuja ga sabbin jakadu

Wanzar da zaman lafiya haƙƙi ne a kanku, cewar Hukumar Abuja ga sabbin jakadu

Daga FATUHU MUSTAPHAMinistan Anuja, Malam Muhammad Musa Bello, ya yi kira ga sabbin jakadun Nijeriya da su kasance masu isar da saƙon zaman lafiya ga 'yan Nijeriya mazauna inda aka tura kowannensu. Ministan ya yi wannan kira ne a lokacin da ya karɓi baƙuncin jakadun a ofishinsa a matsayin wani ɓangare na cika sharuɗɗan matsayin da aka ba su. Da yake jawabi, Bello ya nusar da jakadun kan cewa Birnin Tarayya na nuni da haɗin kan da Nijeriya ke da shi ne, tare da tunatar da su taken bikin cikar Nijeriya shekara 60 da samun 'yancin kai da ya gabata…
Read More
Kwaɓa da harigido ne matsalar mawaƙan wannan zamani – inji Baban Khausar

Kwaɓa da harigido ne matsalar mawaƙan wannan zamani – inji Baban Khausar

Daga AISHA ASAS Malam Sagir Baban Khausar shahararren mawaƙin Hausa wanda waƙoƙinsa suka fi mayar da hankali fannin ilimantarwa, faɗakarwa da nuni cikin nishaɗi. A wannan makon jaridar Manhaja ta samu damar tattaunawa da shi don kawo wa masu karatu wani abu da ba su sani ba game da shi. Ga dai yadda wakiliyar ta tattauna da shi: Mu fara da jin tarihin ka.Assalamu alaikum. Da farko dai suna na Sagir Mustapha Ɗanyaro, jama’a sun fi sani na da Sagir Baban Kausar. Ni haifaffen Lungun Liman ne da ke gidan Liman a Kabala Coastain da ke ƙaramar hukumar Kaduna ta…
Read More
Korona ta yi ajalin mutum milyan biyu a faɗin duniya – Bincike

Korona ta yi ajalin mutum milyan biyu a faɗin duniya – Bincike

Daga WAKILIN MU A halin da ake ciki, adadin mutanen da cutar korona ta aika lahira a faɗin duniya ya kai milyan 2,441,917 kamar yadda sakamakon binciken Jami'ar Johns Hopkins ya nuna. Haka nan, jami'ar ta ce adadin waɗanda aka tabbatar sun kamu da cutar a sassan duniya ya kai milyan 110.3. Sai dai, sakamakon binciken jami'ar ya nuna an samu raguwar adadin mutanen da kan kamu da cutar a cikin yini a faɗin duniya. Inda ya nuna a Talatar da ta gabata aka samu mafi ƙarancin adadi na waɗanda ke kamuwa da cutar a yini. A cewar jaridar Wall…
Read More
Ina daga cikin mutanen farko da su ka kafa Kannywood – Zainab Ahmad

Ina daga cikin mutanen farko da su ka kafa Kannywood – Zainab Ahmad

Hajiya Zainab Ahmad mace ce mai kamar maza kuma ‘yar gwagwarmaya da fafutikar nema wa marasa ƙarfi ko galihu haƙƙin su a wajen waɗanda su ka tauye ma su haƙƙin, da kuma kiraye-kiraye ga Gwamnati da tunasar da ita akan haƙƙin da ya rataya a wuyan ta, musamman ma a Arewacin Nijeriya inda ake fama da matsanancin rashin tsaro. Hajiya Zainab Ahmad ta yi fice a ɓangaren ayyukan agaji da taimakon al’umma wajen shige musu gaba don kwato ‘yancin su. Ga dai hirar da wakiliyar Manhaja ta yi da ita: Daga AISHA ASAS Mu fara da jin tarihin ki a…
Read More
Addini da siyasa: Tsakanin maguzanci da Musulunci a ƙasar Kano (3)

Addini da siyasa: Tsakanin maguzanci da Musulunci a ƙasar Kano (3)

Daga FATUHU MUSTAPHA Ci gaba daga makon jiya A makon da ya wuce mun ji yadda Sarakunan Bagaudawa da haɗin kan malaman Musulunci suka haɗu suka yi wa Tsumburbura korar kare, mun kuma ji yadda har suka yi mata rakiya har sai da ta bar musu gari. To a wannan makon za mu ji kuma, shin mai ya biyo bayan wannan dambarwa da aka shafe ɗaruruwan shekaru ana fafatawa? Kamar dai yadda muka faɗa a wancan makon, Musulunci ya yi nasara a kan maguzanci, to amma kuma wannan nasara da ya yi bai kuma sanya mutanen Kano sun amin ce…
Read More
Delta: Haɗarin mota ya ci jarirai 2 da wasu mutum 4

Delta: Haɗarin mota ya ci jarirai 2 da wasu mutum 4

Daga FATUHU MUSTAPHA Wani mummunan haɗari da ya auku a jihar Delta, ya ci ran jarirai biyu da na wasu mutum huɗu. Haɗarin ya auku ne a ranar Alhamis a kan babbar hanyar Asaba zuwa Ughelli cikin ƙaramar hukumar Oshimili ta Arewa. Bayanai sun nuna haɗarin ya auku ne a sakamakon aikin gyaran hanyar da ke gudana a yankin wanda hakan ya tilasta abubuwan hawa yin amfani da gefe ɗaya na hanyar. Sai dai wasu da abin ya faru a gabansu, sun ce gangacin direbobin da haɗarin ya rutsa da su na daga cikin dalilin da suka haifar da aukuwar…
Read More
Ƙungiyar GCAF ta samu nasarorin tallafa wa mabuƙata da dama, inji Ambasada Ɗanlarabawa

Ƙungiyar GCAF ta samu nasarorin tallafa wa mabuƙata da dama, inji Ambasada Ɗanlarabawa

Gidauniyar Tallafa wa mabuƙata daga tushe (wato Grassroot Care and Aid Faudation) gidauniya ce da ta dukufa wajen ayyukan jinƙai musamman a Arewacin ƙasar nan, a wannan tattaunawa da muka yi da shugabanta Ambasada Auwal Muhammad Ɗanlarabawa za ku ji irin faɗi tashin da wannan Gidauniya ta yi cikin shekaru 10 da kafuwarta ku biyo mu donmin jin yadda tattauawar mu za ta kasance: Daga IBRAHIM HAMISU KANO Masu karatun mu za su so sanin cikakken sunan ka da taƙaitacen tarihin ka?Suna na Ambasada Auwal Muhammad Ɗanlarabawa an haife ni a Gama dake Ƙaramar Hukumar Nassarawa a Jihar Kano, anan…
Read More
Samar da ilimi da cigaban rayuwa: Yadda Abdulnaseer Bobboji ya taka rawar gani a Jalingo

Samar da ilimi da cigaban rayuwa: Yadda Abdulnaseer Bobboji ya taka rawar gani a Jalingo

Daga MUKHTAR YAKUBU a Jalingo A rayuwar duniya ta wannan lokaci, babu wani abu da a ke buƙatar ɗan Adam ya samu kamar ilimi na zamani da kuma na addini. Wannan ya sa ƙasashen da suka cigaba sika ɗauki ɓangaren ilimi da muhimancin gaske ta yadda su ke ba shi kyakyawar kulawar da ta dace, domin kuwa ana samun al'umma masu cigaba ta hanyar bunƙasar iliminsu ta kowanne ɓangare. Domin masana sun ce babu wata al'umma da za ta ci gaba tana cikin duhun jahilci, don haka ne duk wata gwamnati walau ta tarayya ko ta ƙaramar hukuma da ta…
Read More
Gumi ya shiga tsakani don neman kuɓutar da ɗaliban Kagara da aka sace

Gumi ya shiga tsakani don neman kuɓutar da ɗaliban Kagara da aka sace

Daga AISHA ASAS Alamu da dama kuma masu gamsarwa sun nuna fitaccen malamin addinin Islama Sheikh Ahmed Gumi, ya shiga tsakani domin kuɓutar da ɗaliban nan su 27 da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su a Kagara, Jihar Neja, cikin wannan makon. Bayanai daga jihar Neja sun tabbatar da Sheikh Gumi ya ziyarci Neja ya samu ganawa da 'yan bindigar da suka kwashe ɗaliban a dajin Bangi a ranar Alhamis. Idan da dai za a iya tunawa, a daren Larabar da ta gabata 'yan bindigar suka kai hari a Kwalejin Kimiyya ta Gwamnati da ke Kagara a yankin ƙaramar…
Read More